Connect with us

Ƙasashen Waje

Mutane 7 sun ɓace bayan hatsarin jiragen helikwaftan sojin Japan

Published

on

Jami’ai sun ce mutane bakwai ne suka ɓace tun bayan da wani hatsari ya faru cikin dare, wanda ya rutsa da jirage biyu samfurin helikwafta na sojin Japan a tsakiyar teku.

Wani kakakin Hukumar Tsaron-Kai ta Japan (SDF), ya tabbatar wa da kamfanin dillancin labarai na AFP a maraicen Asabar, cewa hatsarin ya faru, inda ya ce an ceto mutum guda.

Ministan Tsaro na Japan, Kihara Minoru ya ce masu ceto “sun gano abubuwan da suka yi kama da ɓangaren jirgin saman a cikin teku, kuma sun yi imani jiragen biyu sun yi hatsari.”

Kihara ya faɗa wa maneman labarai cewa, “A daidai yanzu, ba a san musabbabin hatsarin ba, amma muna iya ƙoƙarinmu don ceto rayuka”.

Alamu sun nuna cewa jiragen helikwaftan sun yi hatsari ne yayin wani atisaye na cikin dare, gab da tsibirin Izu da ke tekun Pacific, a cewar rahotannin gidan jaridar NHK.

KU KUMA KARANTA: Babban Hafsan Sojojin Kenya, Francis Ogollaya, ya mutu a hatsarin helikwafta

Rahotan NHK ya nuna cewa sadarwa da ɗaya cikin jiragen ta katse ne da ƙarfe 10:38 na yamma (13:38 GMT) kusa da tsibirin Torishima, sannan minti ɗaya bayan nan an samu sanarwar gaggawa daga wannan jirgin.

Bayan kamar minti 25, da wajen ƙarfe 11:04 na yamma, sojojin sun gano cewa sadarwa da ɗayan jirgin ta katse shi ma a dai wuri ɗaya.

Jiragen helikwafta ƙirar Mitsubishi SH-60K daga Rundunar Ruwa ta Tsaron-Kai (MSDF) sun fi yin aiki ne kan jiragen ruwan yaƙi.

NHK ta ƙara da cewa, hukumar MSDF ta ce babu wani jirgin sama ko na ruwa a kusa da wajen, kuma ba a tunanin akwai hannun wata ƙasa a hatsarin.

Japan tana ƙara kashe kuɗaɗe wajen harkokin tsaro, kuma tana zurfafa haɗin gwiwa tare da Amurka da sauran ƙasashe a nahiyar Asiya, don martani kan ƙaruwar nuna ƙarfi da China ke yi a yankin, da kuma barazanar da Koriya ta Arewa ke nunawa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Published

on

Isra'ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza, inda ta tilasta wa ɗaruruwan Falasɗinawa tserewa bayan da soji suka kuma ba da umarnin ƙaurace wasu yankuna masu yawan jama’a.

KU KUMA KARANTA: Sojojin Isra’ila sun ce an yi musayar wuta da dakarun Masar

Waɗanda suka shaida lamarin sun ce an kai hari da dama a ciki da wajen birnin Khan Younis, inda aka hallaka mutane takwas kuma mutane sama da 30 suka samu raunuka, cewar wata majiyar lafiya da kuma ƙungiyar Red Crescent ta Falasɗinawa.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC

Published

on

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana - COPEC

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC

Ƙungiyar Kare Haƙƙin Masu Amfani da Man Fetur a Ghana ta yi hasashen cewa akwai yiwuwar a samun ƙarin farashin man fetur a ƙasar a farkon watan Yulin 2024.

Ƙungiyar ta Chamber for Petroleum Consumers (COPEC) ta ce akwai alamu masu ƙarfi da ke nuna cewa farashin fetur da man dizel da gas zai ƙaru baki ɗaya a gidajen man da ke faɗin ƙasar, kamar yadda kamfanin watsa labarai na ƙasar Ghana ya ruwaito.

COPEC ɗin ta ce za a samu ƙarin farashin ne sakamakon yadda farashin Cedi ɗin a ƙasar ke ƙara karewa idan aka kwatanta da dalar Amurka.

COPEC ɗin ta yi hasashen cewa farashin man fetur ɗin wanda za a rinƙa sayarwa a gidan mai zai ƙaru da kashi 2.17 cikin 100, wanda hakan ke nufin zai ƙaru daga Cedi 14.17 zuwa Cedi 15.20 a duk lita.

Sai kuma farashin dizel ana sa ran ya ƙaru zuwa 15.21 a kowace lita ɗaya, sai kuma na gas ya koma tsakanin Cedi 13.24 zuwa Cedi 14.64 a duk kilo ɗaya.

KU KUMA KARANTA: Ɗan Ghana ya kafa tarihi na rungumar bishiyoyi a duniya

Ƙungiyar ta COPEC ta bayar da shawara ga gwamnatin Ghana da ta yi duk mai yiwuwa domin rage harajin da yake a kan gas ko kuma yin tallafi a farashinsa domin bayar da dama ga ‘yan ƙasar su same shi a farashi mai rahusa.

Ta kuma yi ƙira ga gwamnati da kada ta yi ƙasa a gwiwa wajen dawo da matatar mai ta Tema a kan aiki (TOR) don kaucewa ko kuma rage shigo tattacen man fetur wanda a wani lokacin ake samun gurɓatacce.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

An kammala zagayen farko na zaɓen shugaban ƙasa a Iran

Published

on

An kammala zagayen farko na zaɓen shugaban ƙasa a Iran

An kammala zagayen farko na zaɓen shugaban ƙasa a Iran

Daga Ibraheem El-Tafseer

Me magana da yawun Shelkwatar zaɓe ta Iran Dakta Muhsin Elsami, ya sanar da cewa, an kammala lissafi ƙuri’a Miliyan 25 na zaɓen shugaban ƙasar Iran wanda aka fara ranar juma’a.

‘Yan takara 6 ne suka tsallake matakin ƙarshe yayin da 2 suka fice saboda ra’ayin kai, ana zaɓe saura kwana 2.

Dakta Mas’ud Pezeshkian shi ne kan gaba da ƙuri’a Miliyan 10.415.991

Dakta Sa’ed Jalili ya samu ƙuri’u Miliyan 9.473298

Se kuma Dakta Qalibaf ya samu ƙuri’a Miliyan 3.383.340

Sai Ayatullah Musfata ya samu ƙuri’a 206.397.

Yanzu haka an fitar da Dakta Baqir Qalibaf da Ayatullah Musfata da suke da ƙarancin ƙuri’a, ya rage saura Dakta Jalili da Dakta Mas’ud Pezeshkian da ken gaba.

KU KUMA KARANTA: Iran ta tabbatar da mutuwar shugaban ƙasar, Ebrahim Ra’isi, a hatsarin jirgin sama

Jami’i Muhsin Elsami ya sanar da cewa za’a shiga matakin zaɓe na 2 ranar Juma’a mai zuwa inda za a kara tsakanin Dakta Jalili da Dakta Mas’ud.

Cikin su duk wanda ya samu kaso 50 ya zama shugaban ƙasar Iran, wanda zai maye gurbin Shahid Ebrahim Ra’isi wanda ya rasu sanadiyyar hatsarin jirgin Helikofta, a watan da ya gabata.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like