Connect with us

Labarai

Mutane 56 da aka kama aka yi garkuwa dasu a garin Kafin Koro, an ba da wa’adin biyan kuɗin fansa

Published

on

Wasu mutane 56 da aka yi garkuwa da su a ƙauyen Kaffin-Koro da ke ƙaramar hukumar Paikoro a jihar Neja sun yi kukan neman agaji a wani faifan bidiyo da ɓarayin suka fitar.

Jaridar DAILY NIGERIAN  ta rawaito cewa a ranar 10 ga watan Mayu, ‘yan ta’addan sun aukawa garin Kaffin-Koro inda suka yi garkuwa da mazauna garin 56, waɗanda galibinsu manoma ne da ‘yan kasuwa.

DAILY NIGERIAN ta rawaito cewa wasu daga cikin waɗanda abin ya shafa an sako su bayan iyalansu sun biya kuɗin fansa ga ‘yan ta’addan.

Wata majiya da aka sako ‘yan uwanta kwanan nan daga sace su ta tabbatar da biyan kuɗin fansa da dangin suka yi.

“Mun biya Naira miliyan 7.5 kafin a sako ‘yan uwanmu a ranar Litinin”, majiyar da ta nemi a sakaya sunanta ta ce.

A cikin faifan bidiyon da DAILY NIGERIAN ta samu, an ga ‘yan bindigar suna zaluntar waɗanda aka kama tare da yin barazanar kashe su.

Wasu daga cikin waɗanda suka yi garkuwa da su, an ɗaure su ne da sarƙa a ƙafa, yayin da matan da aka yi garkuwa da su aka bar su a tsaye, kuma ‘yan ta’adda masu riƙe da bindigogi sun kewaye su.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mata biyu, shugabannin jam’iyyar APC a Kaduna

‘Yan ta’addan da suka fito da yawa a cikin faifan bidiyon duk suna ɗauke da bindigogi ƙirar AK-47.

A ɗaya daga cikin faifan bidiyon, wani ɗan fashi ya harbi ƙafafun wanda aka kama domin nuna muhimmancin biyan kuɗin fansa.

Haka kuma an ga wani ɗan ta’addan yana nuna wata mata da ke neman a taimaka masa da bindiga ya harbeta, amma bai yi nasara ba.

An kuma ga wani dattijo, mai ɗauke da rauni a ɗaɗɗaure da sarƙa a ƙafa yana jan ƙafa a ɗaya daga cikin bidiyon.

An ce ‘yan fashin sun ba da wa’adin ga iyalan waɗanda abin ya shafa su biya kuɗin fansa ko kuma su rasa ‘yan uwansu.

Wani mazaunin garin Kaffin Koro da ya zanta da wakilinmu da ya nemi a sakaya sunansa ya ce tun lokacin da aka fitar da bidiyon al’ummar yankin sun jefa al’ummar yankin cikin firgici.

“Bidiyon ya yaɗu kuma ya kasance abin tattaunawa a cikin al’umma, amma ban iya kallon shi ba saboda ‘yar’uwata ta kasance a cikin waɗanda aka kashe.

Mutane da yawa sun iya gano ‘yan uwansu a cikin wannan mugunyar bidiyo,” in ji shi.

Da aka tuntuɓi jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Biodun Wasiu, ya ce ‘yan sandan na aiki tare da haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da jihohi maƙwabta domin ceto waɗanda lamarin ya rutsa da su.

“Muna aiki da sauran hukumomin tsaro, musamman sojoji, kuma muna haɗin gwiwa da sauran jihohin da ke maƙwabtaka da su don ganin an kuɓutar da su daga hannun waɗanda ake garkuwa da su,” in ji Mista Abiodun.

Babban sakataren yaɗa labarai na gwamnan jihar, Bologi Ibrahim, bai mayar da martani ga saƙon SMS da aka aike zuwa layinsa ba a lokacin da aka gabatar da wannan rahoto.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Published

on

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Daga Idris Umar, Zariya

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce za ta maka jaridar Daily Trust a kotu, tare da shigar da ƙorafi game da ita, a gaban ƙungiyar masu gidajen jarida ta Najeriya saboda abin da ta ƙira ”yaɗa kalaman neman tayar da rikici da karya aikin jarida”

Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris ya ce gwamnatin tana sane da yadda a cikin ‘yan watannin baya, jaridar Daily Trust ke yaɗa labaran da ke neman gogawa gwamnatin kashin kaji.

Da ya ke magana a wajen wani taron manema labarai a ranar Asabar, ministan yaɗa labaran ya kafa hujja da labaran da jaridar Daily Trust ta wallafa a game juyin mulkin Nijar, da wanda ya ce jaridar ta rubuta a kan shirin sauya sunan titin Murtala Muhammad da ke Abuja zuwa Wole Soyinka da kuma na baya bayan nan a game da sanya hannu a kan yarjejeniyar da ta shafi amincewa da auren jinsi.

KU KUMA KARANTA: Alaƙar soyayya tsakanin jinsi ɗaya ta haramta a Iraƙi

Ya yi bayanin cewa a dukkan labaran, gwamnatin ta gano yadda jaridar ta bayar da rahoto ba tare da gabatar da hujja ko shaidun zargin da ta yi ba, lamarin da kuma gwamnatin ke kallo a matsayin wani yunƙuri na wallafa ƙarya domin tunzura jama’a.

Ya ce: ‘’Ba mu taɓa tunanin Daily Trust da mutanen da ke da ita za su kai wannan mataki ba wajen neman tayar da rikici a ƙasar nan, ta hanyar zargin cewa gwamnati ta sanya hannu a kan yarjejeniyar tallata auren jinsi. Wannan tsabar zalunci ne saboda babu wannan tanadi a cikin yarjejeniyar.’’

Ministan ya koka da yadda wannan labarin ya janyo huɗuba mai zafi daga wasu malaman addini da kuma jefa jama’a cikin halin ɗarɗar, wanda kuma ya ce jaridar ce ta janyo.

KU KUMA KARANTA: Malaman addini a Malawi sun yi zanga-zangar nuna rashin amincewa da auren jinsi

Saboda haka, ministan ya ce ‘’Gwamnatin tarayya za ta bi duk hanyoyin da doka ta amince da su, domin neman haƙƙi a kotu.’’

Continue Reading

Labarai

Gwamnan Neja ya ba da umarnin a mari malamin addini (Bidiyo)

Published

on

Gwamnan Neja ya ba da umarnin a mari malamin addini (Bidiyo)

Gwamnan Neja ya ba da umarnin a mari malamin addini (Bidiyo)

An jiyo Gwamna Mohammed Umaru Bago na jihar Neja yana ba da umarnin jami’an tsaronsa da su yi wa wani malamin addinin Islama cin mutunci a yayin bikin addu’ar Fidda’u ga matar mataimakinsa, Hajiya Zainab Yakubu Garba da ta rasu.

Lamarin wanda ya auku a Minna a ranar Juma’a, ya auku ne a lokacin da malamin ya sadaukar da kansa domin gudanar da addu’a, lamarin da aka ce ya harzuƙa Gwamna Bago.

A cikin faifan bidiyon, ana iya jin Gwamna Bago yana jawabi ga masu jajantawa, inda ya nuna cewa za a iya gudanar da addu’o’i ga marigayiyar a cikin gida, kafin daga bisani ya fusata a lokacin da malamin ya fito.

KU KUMA KARANTA: Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Ya tuhumi malamin, sannan ya umurci jami’an tsaronsa da su ɗauki mataki, inda ya umarce su da su yi masa mari mai kyau sannan su kama shi.

Shaidu da suka halarci taron sun nuna kaɗuwa dangane da wannan hali na gwamnan, inda suka yi la’akari da irin tsaurin ra’ayinsa ga malamin.

Wannan lamari dai ya ƙara rura wutar zarge-zargen da ke tattare da yadda Gwamna Bago ke da alaƙa da cin zarafi ga mataimaka da magoya bayansa, kamar yadda SaharaReporters ta ruwaito kuma majiyar gwamnan ta tabbatar.

Kalli bidiyon a nan:

Continue Reading

Labarai

ECOWAS na shirin ƙaddamar da kuɗin bai ɗaya da zai yi aiki a ƙasashen ƙungiyar

Published

on

ECOWAS na shirin ƙaddamar da kuɗin bai ɗaya da zai yi aiki a ƙasashen ƙungiyar

ECOWAS na shirin ƙaddamar da kuɗin bai ɗaya da zai yi aiki a ƙasashen ƙungiyar

Ministocin kuɗi da Gwamnonin manyan Bankunan ƙasashen ƙungiyar raya tattalin arzikin Yammacin Afirka 15, sun ci gaba da shirye-shiryen ƙaddamar da kuɗin bai ɗaya da aka yiwa laƙabi da ECO.

Wannan yunƙuri da ke da nufin haɓaka tattalin arziƙi yankin Afirka ta Yamma, ya samu amincewar tarayyar Najeriya.

A wata sanarwa da ma’aikatar kuɗi ta Najeriyar ta fitar jiya juma’a, ɗauke da sa hannun Daraktan watsa Labarai, Mohammed Manga, ta ce Ministan Kuɗin ƙasar Wale Edun, ya lura da muhimmiyar rawar da kuɗin na bai ɗaya zai taka wajen bunƙasa ci gaban tattalin arziƙi, da kuma ci gaban yankin baki ɗaya.

KU KUMA KARANTA:ECOWAS na buƙatar dala biliyan 2.6 duk shekara don kafa rundunar tsaro – Badaru

Edun, ya kuma jaddada ƙudirin Najeriya na ci gaba da shiga gaba wajen aiwatar da shi, wanda ake ganin wani ɓangare ne daga shirin hukumar yin katin ɗan ƙasa na samar da kati guda mai amfani a wurare uku, wanda ake sa ran zai fara aiki a watan Agusta mai zuwa.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like