No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wata motar bas da ke jigilar galibin baƙin haure ‘yan ƙasar Venezuela ta yi hatsari a tsakiyar ƙasar Mexico a ranar Talata, inda aƙalla mutane 15 suka mutu sannan wasu 36 suka jikkata, kamar yadda hukumomi suka bayyana.

Motar ta yi karo da wata tirela a kan babbar hanyar da ta haɗa jihohin Puebla da Oaxaca, gwamnatin Puebla ta bayyana a dandalin sada zumunta na X, wanda a da ake ƙira Twitter.

“Abin takaici mutane 15 ne suka rasa rayukansu sannan wasu 36 suka jikkata,” in ji ta. Gwamnan Oaxaca, Salomon Jara, ya ce ya umarci hukumomi a jihar ta Kudu da su ba da tallafi ga waɗanda suka jikkata.

KU KUMA KARANTA: Aƙalla mutane 18 ne suka jikkata a Sri Lanka sakamakon hatsarin motar bas

“Muna aika ta’aziyya ga iyalan mamacin,” kamar yadda ya rubuta a shafukan sada zumunta.

Mummunan haɗurran tituna sun zama ruwan dare a Meziko, galibi saboda tsananin gudu, rashin yanayin abin hawa ko gajiyawar direba.

Irin waɗannan haɗarurrukan ne ke haddasa mace-mace tsakanin ‘yan ci-rani da ke tafiya mai hatsarin gaske zuwa Amurka.

A farkon watan Agusta, aƙalla mutane 18 ne suka mutu a lokacin da wata motar bas ɗauke da baƙin haure da ‘yan ƙasar Mexico suka kutsa cikin wani ƙwarin da ke jihar Nayarit da ke arewa maso yammacin ƙasar.

A watan Fabrairu, baƙin haure daga Venezuela, Colombia, da Amurka ta tsakiya sun yi hatsarin motar bas a tsakanin jihar Oaxaca da ke kudancin ƙasar da kuma tsakiyar Puebla wanda ya yi sanadin mutuwar aƙalla mutane 17.

A watan Yuli, aƙalla mutane 29 ne suka mutu a lokacin da wata motar fasinja ta kutsa daga kan titin tsaunuka ta faɗa cikin wani rafi a Oaxaca.

A watan Disambar 2021, wata tirela ɗauke da baƙin haure 160 ta faɗa kan wata gadar masu tafiya a ƙafa a kan wata babbar hanya a jihar Chiapas da ke kudancin ƙasar, inda mutane 56 suka mutu, galibi ‘yan ƙasar Guatemala.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...