Connect with us

Labarai

Muna zuba jari a ɓangaren fasaha domin yaƙi da cin hanci – Tinubu

Published

on

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya bayyana cewa gwamnatinsa na zuba jari matuƙa a ɓangaren fasaha wadda za ta taimaka wurin kawo ci gaba ga gwamnatin Najeriya.

Shugaban ya bayyana haka ne a lokacin wata tattaunawa da shugaban kamfanin Microsoft wato Bill Gates, bayan sun haɗu a birnin Riyadh na Saudiyya a ranar Lahadi.

Shugaban ya bayyana cewa fasaha ta kasance wani makami da ake amfani da shi domin yaƙar cin hanci da rashawa da kuma yaƙar yadda ake wadaƙa da kuɗaɗen al’umma.

Tinubu ya jaddada cewa ana samun turjiya daga wurin al’umma a yunƙurin da ake yi na amfani da fasaha wurin kawo ci gaba.

KU KUMA KARANTA: Ta’addanci babbar masifa ce da aka shigo da ita Afirka daga waje – Shugaba Tinubu

“Fasaha abokiyar gaba ce ga cin hanci da aikata ba daidai ba. Muna ta aiki tuƙuru domin inganta fasaha,” in ji Shugaba Tinubu.

Shugaban ya bayyana cewa lokacin da yake gwamnan Legas, ya yi amfani da fasaha domin tattara bayanai da kuma amfani da su wurin karɓar haraji, wanda hakan ya samar da tsari mai kyau na karɓar haraji.

A martanin da ya mayar, Mista Gates ya shaida wa shugaban ƙasar kan cewa akwai wata manhaja ɗaya wadda za a iya amfani da ita wurin haɗe bayanai da suka shafi tsare-tsare da tsaro da kuma kula da haraji.

“Muna aiki tare da Mista Wale Edun, wanda shi ne Ministan Tattalin Arziki da Kuɗi kan batun fasahar zamani. Kafin ka karɓi mulki, akwai wasu abubuwa kaɗan da aka yi ƙoƙarin haɓaka manhajar tattara bayanai. Sai dai an bar su sun warwatsu. Akwai manhajoji da dama na tantance bayanan mutane.

“A yanzu akwai shirin da ake yi na amfani da fasahar nan ta MOSIP wurin tattara bayanai ta yadda jama’a za su iya samun abubuwansu ta yanar gizo. Za mu iya taimakawa ta wannan ɓangaren kuma za mu iya bayar da ƙarin taimako,” in ji Bill Gates.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like