Connect with us

Labarai

Muna so gwamnati ta fara biyan mu albashi – masu gadin maƙabartu a Yobe

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Masu kula ko kuma masu gadin maƙabartu a jihar Yobe, sun yi ƙira ga gwamnatin jihar Yobe, da ta taimaka ta fara biyansu albashi. Sun yi wannan ƙiran ne a lokacin da Neptune Hausa ta ziyarci wasu daga cikin maƙabartun a garin Potiskum, domin ganin irin yadda ruwa ya mamaye wasu maƙabartun, wanda hakan ya yi sanadiyyar rubzawar ƙabarurruka da yawa a daminar da ta gabata.

Neptune Hausa ta zanta da Malam Adamu Yawale, ɗaya daga cikin masu gadin maƙabartar bayan Asibitin ƙwararru da ke Potiskum (Yobe State Specialist Hospital, Potiskum). Ya shaida wa wakilinmu cewa “A wannan maƙabarta, muna fama da matsaloli, musamman na rubzawar ƙaburbura, kuma babu ƙasar cuko. Muna so gwamnati ko wasu al’umma su taimaka su kawo mana ƙasa don mu cike ƙaburburan da suka rubza.

Sannan muna tsananin buƙatar itace na buso a wannan maƙabarta. Lokuta da dama sai an kawo za a binne mutum, amma babu itacen da za a saka kabari wanda za a binne mutum da shi. Dole sai dai ‘yan’uwan mamacin su fita su je su sayo itacen, kafin a binne mutum”.

KU KUMA KARANTA: Tinubu ya ba da umarnin biyan malaman jami’a albashin watannin da suka yi suna yajin aiki

Malam Adamu, ya ƙara da cewa “kullum a wannan maƙabarta muke wuni. Mune muke kula da ita, mune muke tona ƙaburburan da ake zuwa ake binne bayin Allah. Ba ma samun abin kashewa, da na cefane ga iyalanmu, sai dai idan an kawo jana’iza, idan jama’a sun taimaka mana da sadaka, sannan muke samun ɗan wani abu”.

Malam Sulaiman Sa’id, ɗaya ne daga cikin masu gadin maƙabartar Mamman B. Ali, wadda aka fi sani da maƙanartar MAL. Ya shaida wa wakilinmu cewa “wannan maƙabarta, ta fi kowace maƙabarta girma a garin Potiskum. Amma duk girmanta wannan maƙabarta, ba ta da hanyar ruwa, ka ga kuwa idan wuri ya yi girma kuma babu hanyar ruwa, to dole ne wurin ya nashe. Ta haka yake samun dama ya je ya shiga kabarurruka, ya rubzasu. Duk kyan aikinku a wannan maƙabarta, sakamakon rashin hanyar ruwa, sai ruwan ya je ya rusa kabarurruka.

Babban abin da muke buƙata shi ne gwamnati ta zo ta cire mana hanyar ruwa guda biyu ko uku, wanda ruwan zai samu hanyar fita waje. Sannan muna tsananin buƙatar itace a wannan maƙabarta. Kusan dukkan ƙauyukan kusa damu, nan maƙabartar suke kawo jana’iza. Ana kawo jana’iza 20 zuwa 30 a kullum a wannan maƙabarta. To wannan ne yake sa wa duk yawan itacen da aka kawo wannan maƙabarta yake yawan ƙarewa. Babu shakka jama’a suna taimaka wa da itace, amma yawan jana’iza da ake kawo wa, shi ne yake kawo ƙarewar itacen da wuri.

Sannan buƙata ta gaba shi ne, muna so gwamnati ta fara biyanmu albashi. A iya sanina, a dukkan maƙabartu na garin Potiskum, waɗanda gwamnati take iya biyansu albashi, mutane biyu ne. Gwamnati ba ta biyan mutanenmu masu kula da dukkan maƙabartu kuɗi don su dinga ciyar da iyalansu. Muna so gwamnati ta dube mu da idon rahama, ta dinga biyanmu albashi, don mu dinga samun abin da za mu ciyar da iyalanmu”. inji shi.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like