Connect with us

Labarai

Muna cikin fargabar rasa gidajenmu – mazauna unguwar Kwari Potiskum

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Al’ummar da suke zaune a unguwannin Kwari, Batayya da Kusa da Gadar hanyar Kano dake garin Potiskum jihar Yobe, sun koka a kan yadda suke fuskantar barazanar ruwan sama na zabtarewa haɗe da rushewar gidajensu. Jama’ar wannan yanki sun shafe shekara da shekaru ruwan yana musu barazana, wasu kuma tuni har sun tashi sun bar muhallan nasu, sakamakon ruwan ya cinye gidajen nasu gabaɗaya.

Waɗanda wannan barazanar zabtarewar gidajen ya fi shafa, sune waɗanda gidajen su yake kusa da hanyar da ruwan yake wucewa. Duk lokacin da ake ruwan sama, to su fa al’ummar wannan unguwannin hankalinsu ba a kwance yake ba. Wasu ma tashi suke su bar unguwar, sai an gama ruwan sannan su dawo.

Wakilinmu ya shiga unguwar, kuma ya gane wa idonsa yadda ruwan yake musu barazana. A tattaunawar da ya yi da wasu daga cikin mazauna unguwar sun shaida masa cewa, sun kai kukansu wajen gwamnatin jihar Yobe, ba sau ɗaya ba, ba sau biyu ba. Amma har yanzu gwamnati ba ta waiwayo su ba. Suka ce duk shekara ruwan sai ya cinye gidajen jama’a, sakamakon rashin gyara da gwamnatin ba ta yi ba a hanyar da ruwan yake wucewa.

“Gwamnatin Alhaji Mai Mala Buni, mun je mun koka mata a kan wannan matsala da muke fuskanta na rasa gidajenmu sakamakon rashin gyara a wannan hanyar ruwa, zuwa yanzu dai ba mu ga komai ba. Amma muna zuba ido” inji wani mazaunin unguwar, Malam Salihu Muhammad.

Malam Abbas Hassan, wani mazaunin unguwar ne, kuma wanda wannan zabtarewar gidajen yake masa barazana, ya shaida wa Neptune Hausa cewa “wannan damuna ta bana ina cikin fargaba da matsanancin tashin hankali, domin bai fi saura mita takwas ruwan ya cinye gidana ba. Idan kuma ruwa ya raba ni da gidan nan, to fa ban san inda za mu shiga ni da iyalaina ba. Muna fatan kukanmu zai kai ga kunnen gwamnati” cikin alhini da ban tausayi yake koka wa gwamnatin jihar Yobe halin da suke ciki.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like