Connect with us

Labarai

Mun rasa rayukan mutane 57 a haɗarin kwale-kwale uku, cikin mako ɗaya – Gwamnatin Adamawa

Published

on

Gwamnatin jihar Adamawa ta gano abubuwan da suka haddasa hatsarin kwale-kwale guda uku a jere a jihar cikin mako guda.

Hatsarin ruwa ya yi sanadiyar mutuwar mutane kusan 57 a cikin kwanaki takwas da suka gabata, lamarin da ya janyo suka kan yadda ake tafiyar da harkokin sufurin ruwa a jihar Arewa maso Gabas.

Hatsari na baya bayan nan ya faro ne a ranar Litinin 4 ga watan Satumba, inda wani kwale-kwalen da ke tafiya tsakanin Mayo-Ine da Mayobelwa a ƙaramar hukumar Mayobelwa ya kife, inda fasinjoji biyu suka mutu.

Bayan kwanaki huɗu, wani hatsarin wani kwale-kwalen da ke jigilar ‘yan kasuwa da manoma 23 daga ƙauyen Rugange zuwa garin Yola da ke yankin Yola ta Kudu ya auku a tafkin Njuwa da ke ƙauyen Dandu wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane 15.

KU KUMA KARANTA: Mutane da yawa sun mutu a hatsarin Kwale-kwale a Adamawa

A ranar Litinin ɗin da ta gabata, a daidai lokacin da masu aikin ceto ke ƙoƙarin ƙwato gawarwakin mutanen da suka ɓace daga tafkin Njuwa, wani kwale-kwalen da ke ɗauke da fasinjoji da dama ya kife da wata iska mai ƙarfi a garin Gurin na ƙaramar hukumar Fufore.

Masu ruwa da tsaki na yankin sun ceto mutane 11 yayin da wasu da dama suka ɓata inda aka ƙiyasta mutuwar mutane 40. Sakataren zartarwa na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Adamawa, Muhammad Amin Sulaiman, a ranar Talata ya bayyana yawan lodi, rashin la’akari da rashin amfani da rigunan kare rai a matsayin abubuwan da ke haddasa haɗurran, yana mai cewa gwamnati na ƙoƙarin tabbatar da matakan tsaro don hana aukuwar lamarin nan gaba.

Gwamnan jihar, Ahmadu Umaru Fintiri wanda ya kai ziyarar jajantawa garin Gurin a ranar Talata ya ce ya umurci dukkanin hukumomin da abin ya shafa da su tabbatar da tsaro da suka haɗa da hana lodi fiye da ƙima da kuma amfani da rigar kare rai a cikin ruwa.

Don haka Fintiri ya yi ƙira ga sarakunan gargajiya da kansilolin ƙananan hukumomi da su ba gwamnatinsa goyon baya wajen hana ci gaba da asarar rayuka sakamakon sakaci da kuma rashin mutunta dokokin tsaro.

Ya ce, “Mun zo nan ne domin mu jajanta muku kan yadda mutanenmu suka nutse a nan.

Ina so in jawo hankali ga hatsarori da ke tattare da amfani da kwale-kwale ba tare da rigunan kare rai ko injuna ba don tuƙa shi musamman lokacin haɗari ko ƙasa mai nauyi.

Mu sani rayuwa ta fi kuɗi. “Zan umurci dukkan hukumomin da abin ya shafa da su daidaita harkar sufurin ruwa.

KU KUMA KARANTA: Mutane takwas sun mutu, bakwai sun ɓace, a hatsarin kwale-kwale – Gwamnatin Adamawa

Za mu samar da jaket ɗin kare rai a duk inda ake jigilar mutane. Sarakunan gargajiya su tabbatar da cewa kwale-kwalen da zai iya ɗaukar mutum 10 ya taƙaita ga mutum 10 kawai.

Abin da muka gani a Rugange da Gurin ya isa ya zama darasi a gare mu. Ba za mu jira zuwa ta’aziyya ba bayan asarar rayuka.

Za mu hana shi ba tare da tsoro ko yarda ba.” Wani mai kamun kifi kuma direban kwale-kwale mai suna Ɗanlami Adahnu mai ritaya, ya shaida wa wakilinmu cewa, kwaɗayin masu safarar kaya ne ke haddasa yawaitar tashe-tashen hankula, inda ya ce a lokacin guguwa, mai hikimar kwale-kwale zai rage yawan fasinjojin da ke ƙasa da ƙarfin kwale-kwalen don kaucewa kifewa.

“Hanya mafi kyawun rigakafin haɗari ita ce guje wa yin lodi fiye da kima.

Domin a lokacin damina, igiyoyin ruwa suna da ƙarfi da sauri, don haka mai hankali yakan rage yawan fasinjoji ko da ƙasa da ƙarfin kwale-kwale don gudun ka da ya kife.” Inji Adahnu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Published

on

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Afirka ta Yamma mai rarrabuwan kai ta gudanar da tarukan ƙolin shugabannin ƙasa guda biyu a ƙasashe daban-daban biyu a ƙarshen makon, inda aka gudanar da taro farko ranar Asabar a Nijar tsakanin shugabannin mulkin soja na yankin Sahel.
A gefe guda kuma za a gudanar da wani taron ƙoli ranar Lahadi a Najeriya inda shugabannin sauran ƙasashe mambobin ƙungiyar tattalin arziƙin yankin ta ECOWAS za su hallara.

Taron ƙolin da ake yi yau Asabar a Yamai babban birnin Jamhuriyar Nijar, zai kasance karo na farko tsakanin shugabannin sojojin sabuwar ƙungiyar haɗin kan yankin Sahel wato Alliance of Sahel States ko kuma AES.

Mali, Burkina Faso da Nijar su ne suka kafa yarjejeniyar kare juna a watan Satumba, waɗanda suka bar babbar ƙungiyar ECOWAS a cikin watan Janairu.

Ficewar su daga ECOWAS, wani ɓangaren ya samo asali ne daga zargin da suke yi cewa Paris tana yiwa ƙungiyar katsalandan kana ba ta ba da taimakon da ya kamata a yaƙi da masu iƙirarin yaƙin jihadi.

Ficewar ta sa ƙasashen uku sun janye kansu daga Faransa da ta yi musu mulkin mallaka, suka kori sojojin Faransa masu yaƙi da masu iƙirarin jihadin kana suka juya zuwa ga ƙasashen da suke ƙira da aminan gaskiya, da suka haɗa da Rasha da Turkiya da kuma Iran.

KU KUMA KARANTA:Shugabannin Nijar, Mali da Burkina Faso sun kafa ƙungiyar haɗaka

Idan aka yi la’akari da munanan tashe-tashen hankula na ‘yan jihadi da ƙasashen uku ke fuskanta, “yaƙin da ta’addanci” da “ƙarfafa haɗin gwiwa” za su kasance kan ajandar taron ƙolin na yau Asabar, a cewar fadar shugaban ƙasar Burkina Faso.

Taron ƙolin da za a gudanar ranar Lahadi a Abuja zai ba shugabanni a ƙasashen ECOWAS damar tattaunawa a kan irin alaƙa da za su ƙulla da ƙungiyar ta AES.

Bayan wasu tarurrukan da suke yi tsakanin ƙasashe biyu, shugabannin uku na yankin Sahel sun yi taro a karon farko tun bayan da suka hau karagar mulki ta hanyar juyin mulki tsakanin shekarar 2020 zuwa 2023.

Continue Reading

Labarai

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

Published

on

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

 

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin cewar ‘yan Najeriya miliyan 82, kimanin kashi 64 na ‘yan ƙasar ka iya fuskantar matsalar yunwa nan da shekarar 2030.

Haka kuma MƊD ta yi ƙira da gwamnatin ƙasar ta magance matsalar sauyin yanayi da matsalar ƙwari da sauran abubuwan da yi wa harkar noma barazana.

Jaridun Najeriya sun ambato jami’in Majalisar Ɗinkin Duniyar, Taofiq Braimoh – wanda ya wakilci kodinetan ayyukan jin ƙai na hukumar abinci da ayyukan noma na majalisar na bayyana haka lokacin da yake jawabi kan matsalolin ƙarancin abinci a taron ƙaddamar da shirin bunƙasa ayyukan noma na ‘CropWatch’ a birnin Abuja.

KU KUMA KARANTA:Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi maraba da sakin yara 21 da aka yi garkuwa da su

Mista Braimoh ya ce akwai buƙatar gwamnatin Najeriya ta ɗauki matakan da suka dace cikin gaggawa don magance matsalar.

“Gwamnatin Najeriya tare da haɗin gwiwa masu ruwa da tsaki, sun gudanar da bincike na shekara-shekara da suka saba gudanarwa kan abinci. Sakamakon binciken ya tayar da hankali, kimanin mutum miliyan 82 ne za su fuskanci yunwa nan da 2030,” kamar yadda Jaridun ƙasar suka ambato Braimoh na bayyanawa.

Ya ci gaba da cewa matsalar rashin abinci da ƙasar ke fama da shi, baya rasa nasaba da matsalar sauyin yanayi da duniya ke fama da ita, da matsalar ƙwari da wasu abubuwa da ke yi wa harkar noma barazana a ƙasar.

Hasashen na Majalisar Ɗinkin Duniyar na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasar ke fama da matsalar tsadar abinci, lamarin da ya tilasta wa gidaje da dama haƙura da sayen abincin da suka saba ci.

A cikin rahotonta baya-bayan nan, hukumar ƙididdigar ƙasar ta ce farashin abinci a ƙasar ya ƙaru zuwa kashi 40.66 a watan Mayu, matakin da aka jima ba a ga irinsa ba.

Continue Reading

Labarai

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Published

on

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Daga Idris Umar, Zariya

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce za ta maka jaridar Daily Trust a kotu, tare da shigar da ƙorafi game da ita, a gaban ƙungiyar masu gidajen jarida ta Najeriya saboda abin da ta ƙira ”yaɗa kalaman neman tayar da rikici da karya aikin jarida”

Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris ya ce gwamnatin tana sane da yadda a cikin ‘yan watannin baya, jaridar Daily Trust ke yaɗa labaran da ke neman gogawa gwamnatin kashin kaji.

Da ya ke magana a wajen wani taron manema labarai a ranar Asabar, ministan yaɗa labaran ya kafa hujja da labaran da jaridar Daily Trust ta wallafa a game juyin mulkin Nijar, da wanda ya ce jaridar ta rubuta a kan shirin sauya sunan titin Murtala Muhammad da ke Abuja zuwa Wole Soyinka da kuma na baya bayan nan a game da sanya hannu a kan yarjejeniyar da ta shafi amincewa da auren jinsi.

KU KUMA KARANTA: Alaƙar soyayya tsakanin jinsi ɗaya ta haramta a Iraƙi

Ya yi bayanin cewa a dukkan labaran, gwamnatin ta gano yadda jaridar ta bayar da rahoto ba tare da gabatar da hujja ko shaidun zargin da ta yi ba, lamarin da kuma gwamnatin ke kallo a matsayin wani yunƙuri na wallafa ƙarya domin tunzura jama’a.

Ya ce: ‘’Ba mu taɓa tunanin Daily Trust da mutanen da ke da ita za su kai wannan mataki ba wajen neman tayar da rikici a ƙasar nan, ta hanyar zargin cewa gwamnati ta sanya hannu a kan yarjejeniyar tallata auren jinsi. Wannan tsabar zalunci ne saboda babu wannan tanadi a cikin yarjejeniyar.’’

Ministan ya koka da yadda wannan labarin ya janyo huɗuba mai zafi daga wasu malaman addini da kuma jefa jama’a cikin halin ɗarɗar, wanda kuma ya ce jaridar ce ta janyo.

KU KUMA KARANTA: Malaman addini a Malawi sun yi zanga-zangar nuna rashin amincewa da auren jinsi

Saboda haka, ministan ya ce ‘’Gwamnatin tarayya za ta bi duk hanyoyin da doka ta amince da su, domin neman haƙƙi a kotu.’’

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like