No menu items!

Sample Page Title

Date:

Mun kashe ’yan boko haram 5, 44 sun miƙa wuya – Sojojin Najeriya

Daga Ali Sanni Larabawa

Rundunar Sojin Najeriya, ta sanar da cewar dakarunta sun kashe ’yan ta’adda biyar tare da kama wasu 44 da suka miƙa wuya a jihar Borno.

Wannan na ɗauke ne a  cikin wata sanarwa da rundunar sojin ta fitar a shafinta na X (twitter), a ranar Talata.

A yayin ayyukansu, sojojin sun gano abubuwa masu fashewa, makamai, alburusai, da shanun da aka sace, sannan sun kama wasu masu laifi.

Sojojin, sun bayyana cewa a ranar Litinin, sun kai hari sansanin ’yan ta’addan ISWAP da ke yankin Bama a jihar Borno.

KU KUMA KARANTA: Mayaƙan ‘Boko Haram’ a Borno sun kashe ɗan sanda da ƙona motocin sintiri

A wannan samamen, sun kashe ’yan ta’adda biyar tare da ƙwato wasu abubuwa kamar bam, RPG, bindigogi guda biyu, AK-47, alburusai 23, babura guda shida, da kuma wasu magunguna.

Kazalika, sojojin sun ce sakamakon ci gabada kai hare-hare a yankin Arewa Maso Gabas, ’yan Boko Haram guda 44 da iyalansu sun miƙa wuya ga dakarun a yankunan Bama, Dikwa, da Gwoza na jihar ta Borno.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...