No menu items!

Sample Page Title

Date:

Mun gana da shugaba Tinubu mun isar masa saƙon al’umma – Shaikh Bala Lau

Daga Idris Umar, Zariya

A ranar Alhamis tawagar malaman Najeriya ta gana da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu dangane da halin da ƙasa ta ke ciki kan batun zanga-zanga da wasu ke ƙiran a yi dalilin halin matsi da tsadar rayuwa.

Rahoton sun nuna cewa jim kaɗanne bayan kammala ganawar, shugaban ƙungiyar Izala na ƙasa, Shaikh Abdullahi Bala Lau ya shaidawa manema labarai cewa shugaban ƙasa ya karɓi koken da suka je masa da shi.

“Mun faɗa mar halin da al’umma suke ciki na tsadar rayuwa, taɓarɓarewar tsaro da wahalar rayuwa, ya kuma ce dan Allah a ja hankalin al’umma a ba su haƙuri nan gaba kaɗan za a ga sauyi da gyara kan ƙorafe-ƙorafen da ake yi”. In ji Bala Lau.

KU KUMA KARANTA: Zanga-zanga ba gudu ba ja da baya – ‘Yan Najeriya

Daga nan kuma, Shaikh ɗin ya ja hankalin al’umma da su yi haƙuri su cigaba da addu’a, “ba mu da ƙasar da ta fi Najeriya kar mu rusa ƙasarmu da kanmu”. Inji Shaikh Bala Lau.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...