No menu items!

Sample Page Title

Date:

‘Yan sanda a jihar Kaduna sun ce sun kama wani matashi mai shekara 20, bisa zargin kashe mahaifinsa ta hanyar buga masa taɓarya bayan zuciyarsa ta ƙaddara masa cewa uban na yunƙurin halaka shi.

“Ya shaida mana cewa yana yin mafarke-mafarke, inda yake ganin siffar mahaifin nasa, mai kimanin shekara 50, yana zuwar masa a cikin sigar jemage,” in ji mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar.

ASP Mansur Hassan ya shaida wa manema labarai cewa suna ci gaba da gudanar da bincike kan matashin da suke zargi wanda ya fito daga yankin ƙaramar hukumar Zangon Kataf.

KU KUMA KARANTA: Uwargida ta kwaɗa wa maigida taɓarya a kai, ya mutu har lahira

Ya ce zuwa yanzu ba su samu wata shaida da ke nuna cewa matashin na da wata matsalar kwakwalwa, ko kuma yana shan kayan maye.

Jami’in ‘yan sandan ya ambato matashin na cewa babu kyakkyawar alaƙa tsakaninsa da mahaifin, wanda ya riga mu gidan gaskiya.

‘Yan sandan sun ce da zarar sun kammala bincike za su gurfanar da matashin mai suna David Phillips a gaban kotu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...