Connect with us

Jan hankali

MSSN ta yi ƙorafi ga gwamnatin Najeriya akan rubuce-rubucen jima’i a cikin littattafan ‘yan firamare

Published

on

Ƙungiyar ɗalibai musulmi ta Najeriya (MSSN), ta bayyana damuwarta matuƙa kan sanya rubututtukan jima’i a cikin wasu litattafan firamare da sakandare da ake yaɗawa a Najeriya.

Wasiƙar mai taken “Haɗa Jima’i da Luwaɗi a Littattafan Firamare da Sakandare na Najeriya: Barazana ga ɗabi’a da kai hari kan ɗabi’un al’adu/addini,” an aika zuwa ga ministan ilimi, Adamu Adamu wasiƙar, mai ɗauke da sa hannun shugaban ƙungiyar, Qaasim Odedeji, da babban sakataren ƙungiyar, Abdul Jalil Abdur Razaq, mai ɗauke da kwanan wata 15 ga watan Mayu, ta nuna rashin jin daɗinta kan yadda ake nuna jima’i a wasu litattafan Lissafi, Turanci, da zamantakewa da ake amfani da su a yawancin makarantun sakandaren Najeriya.

“Mun yi mamakin abubuwan da ke cikin wasu litattafan lissafi, Turanci, da Kimiyyar zamantakewa da ake amfani da su a yawancin makarantun sakandaren Najeriya a yau.

KU KUMA KARANTA: Yadda ‘yan bindiga sun kai farmaki makarantar firamare, suka yi awon gaba da ɗalibai

“An lalatar da waɗannan littattafan karatu har sun haɗa da abubuwan lalata da batsa don lalata da yara ƙanana. Da take bayar da misalai, ƙungiyar ta ce tambayar da ake yi wa ɗaliban firamare a fannin lissafi ita ce “kwaroron roba 20 + 5 – robar guda 2 daidai”.

Sun ƙara da cewa wasu daga cikin litattafan suna inganta zubar da ciki, LGBT, al’aura, da jima’i mai aminci. “Mun yi imanin cewa wannan babban cin zarafi ne ga al’adun gargajiya da addinin al’ummar Nijeriya, musamman al’ummar Musulmi.

MSSN, kasancewarta mai ruwa da tsaki a harkar ilimi a Najeriya, za ta iya bayyana tsananin damuwarta da lamarin ba,” inji su.

Sun yi ƙira ga ma’aikatar ilimi da ta gaggauta gudanar da bincike kan lamarin tare da tabbatar da cewa litattafan da ake amfani da su a makarantun Najeriya ba su da abubuwan da ke da illa ga tarbiyyar matasa ɗalibai.

“Muna buƙatar ma’aikatar ilimi ta gaggauta ɗaukar matakin cire duk wasu litattafan da ke ɗauke da abubuwan lalata da ake yaɗawa a makarantun ƙasar nan.

“Mun yi imanin cewa ya kamata tsarin ilimin Najeriya ya kiyaye ɗabi’un, al’adu da addini na al’ummar Najeriya, musamman al’ummar Musulmi,” in ji shi.

Wasu daga cikin littattafan da suka jera sun haɗa da Basic Science Junior Secondary School Razat Publishers, 2018 edition, (na JSS3), New Concept English for Senior Secondary Schools for SSS2, Revised edition (2018 edition), Active Basic Science, 2014 edition, and Basic Science & Fasaha don ƙaramar Sakandare 1, 2 da 3.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Gwamnatin Najeriya ta rabawa mutane 160,572 naira biliyan 14.6 a jihohin arewa shida | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

CBN

Jabun kuɗaɗe sun bazu a gari — CBN

Published

on

Babban Bankin Najeriya (CBN) ya ja hankalin ’yan Najeriya kan jabun takardun kuɗin ƙasar da ke yawo a cikin al’umma a sakamakon raɗe-raɗin da ake yaɗawa na ƙarancin tsabar kuɗi.

Kakakin CBN, Hakama Sidi Ali ta shawarci al’umma da su kasance masu lura ganin cewa masu jabun kuɗaɗe na amfani da su a matsayin kuɗin mota ko a wurin yin cefane da gidajen abinci sauransu.

Sanarwar ta CBN ta ce “Dokar CBN ta tanadi hukucin ɗaurin aƙalla shekaru biyar ga duk wanda ya buga jabun kuɗaɗe.

“CBN na aiki da hukumomin tsaro da na hada-hadar kuɗaɗe wajen ganowa da ƙwace jabun kuɗaɗe da kuma tsare masu buga su.” in ji jami’ar.

Daga nan sai ta umarci bankuna, ’yan canji da sauran cibiyoyin hada-hadar kuɗaɗe da su ɗauki matakan da suka dace wajen ganowa da kuma hana yaɗuwar jabun kuɗaɗe.

Ta ƙara da cewa, “ana ƙira ga jama’a su kai ƙarar duk wanda suka ga yana yin jabun kuɗaɗe ga ofishin yan sanda ko na CBN mafi kusa.

Continue Reading

EFCC

EFCC ta fitar da matakai takwas na kare kai daga masu damfara da katin ATM

Published

on

Hukumar da ke yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin ƙasa zangon ƙasa a Nijeriya, EFCC ta koka kan yadda take yawan samun rahotanni na waɗanda aka cire wa kuɗi daga banki ba tare da saninsu ba kuma akasari ta ATM.

Hukumar ta ce akasarin ƴan damfarar sun fi samun bayanan jama’a ko katin ATM ɗin mutane a wuraren cirar kuɗi na ATM ko kuma masu POS.

EFCC ta yi gargaɗi kan cewa ƴan damfarar suna amfani da katin ATM na bankin mutumin da suke so su yaudara, bayan haka sukan je wurinsa da niyyar taimako idan ya shiga ruɗani a gaban ATM.

Hukumar ta ce ƴan damfarar kan yi sauri su yi wa kwastoman bankin musaya da katinsa bayan su haddace lambobin sirrinsa a lokacin da suke ƙoƙarin taimakonsa, wanda daga baya sai su cire kuɗin da ke asusun ajiyarsa.

Dangane da haka ne hukumar ta fitar da hanyoyi takwas waɗanda take ganin idan jama’a sun bi su za su samu kariya daga masu damfarar:

KU KUMA KARANTA: EFCC za ta gurfanar da sojojin saman Najeriya a kotu kan zargin damfara a intanet

  1. Akwai buƙatar ajiye kati a aminctaccen wuri. Duk lokacin da ka karɓi katinka bayan cire kuɗi, ka tabbata katinka ka karɓa ba wai wanda ke kama da katinka ba.
  2. A rinƙa duba sauran kuɗin da ke asusu (balance) domin dubawa ko an cire kuɗi daga asusu.
  3. Saka ƙararrawa domin lura da duk wani abu da ya shafi asusun ajiya ko katin banki.
  4. Rufe lambobin da ake latsawa a jikin ATM ko POS da hannu a lokacin da ake saka lamobin sirri domin cire kuɗi ko wani amfani.
  5. A rinƙa neman taimako daga jami’an banki, ka da ka yi saurin biyan kuɗi ko cire kuɗi.
  6. A ƙira banki domin toshe katin ATM a duk lokacin da aka lura kati ya maƙale a cikin ATM ko kuma duk lokacin da aka lura da wani lamari wanda yake ba daidai ba.
  7. A tabbata an san lambar da za a iya toshe ATM da ita tare da amfani da ita cikin gaggawa a duk lokacin da aka ɓatar da katin ko aka sace shi.
  8. A latsa lambobin USSD na 966911# da kuma bin matakan da suka biyo baya domin toshe katin ATM nan take.
Continue Reading

Jan hankali

NUJ jihar Yobe, ta nuna rashin jin daɗi da ƙara farashi da masu gidajen mai suka yi

Published

on

Daga Ibraheem EL-TAFSEER

Ƙungiyar ‘yan jarida ta Najeriya (NUJ) reshen jihar Yobe ta bayyana rashin jin daɗin ta game da halin rashin kishin ƙasa da wasu masu gidajen man fetur da ma’aikata suka yi a Damaturu, babban birnin jihar Yobe da sauran ƙananan hukumomin jihar, dangane da ƙarancin man fetur da aka samu a yau da kuma ƙaruwar farashin mai ɗin, wanda hakan ya jawo dogon layi a gidajen man.

A wata takarda da ƙungiyar ta fitar, wanda shugaban ƙungiyar ‘yan jarida na jihar Yobe, Kwamared Rajab Mohammed da sakatatensa Alhassan Sule Mamudo suka sa wa hanu, ta bayyana cewa, ƙungiyar ta damu matuƙa da halin da ‘yan jihar ke ciki masu son zaman lafiya.

KU KUMA KARANTA: Cire tallafin man fetur ya jawo hauhawar farashin mai a Najeriya

Don haka muna ƙira ga hukumomin tsaro, hukumomin gwamnati, hukumomin da abin ya shafa da duk masu ruwa da tsaki da su gaggauta ɗaukar matakan da suka dace don ganin an kawo karshen wannan mummunan yanayi da ke iya lalata tattalin arziƙin al’umma.

Za mu iya kwatanta shi a matsayin zagon ƙasa ga tsarin dimokuraɗiyyar Najeriya. Ƙungiyar za ta ci gaba da sanya ido kan lamarin tare da sanar da ‘yan ƙasar kan duk wani ci gaba mai kyau tare da yin ƙira ga kowa da kowa da su kwantar da hankula domin za a shawo kan lamarin cikin ruwan sanyi.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like