Connect with us

Hatsari

Motar ƴan sanda ta yi hatsari a Kebbi

Published

on

Wata mota ɗauke da jami’an ‘yan sanda zuwa wurin aiki wacce ta taso daga hedkwatar ‘yan sanda SCID a jihar Kebbi ta samu hatsarin da ya yi sanadin mutuwar wani Sufeto na ‘yan sanda.

A wata sanarwa da Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kebbi SP Nafiu Abubakar ya fitar, ya ce hatsarin ya afku ne a sakamakon fashewar taya.

 “An samu mummunan hatsarin mota ɗaya tilo a hanyar Koko/Jega, wanda ya haɗa da motar ‘yan sanda ta Toyota Land Cruiser mai lamba REG. 5465D, ɗauke da tawagar ‘yan sanda ƙarƙashin jagorancin AC CID na rundunar ‘yan sandan jihar Kebbi, ACP Suleiman Saɗe da wasu mutane tara.  

A yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa ziyarar wani wurin da aka aikata laifi a ƙauyen Kendawa, gundumar Dutsinmari a ƙaramar hukumar Koko/Besse.

KU KUMA KARANTA: Hatsarin tirela ya yi ajalin mutum 25 a Neja

Lokacin da suka isa yankin NNPC a garin Koko, ɗaya daga cikin tayoyin motar ya fashe kuma motar ta mirgina sau uku a cikin daji da ke kusa.

Nan take tawagar ‘yan sanda daga sashin Koko suka ziyarci inda lamarin ya faru, inda aka kwashe waɗanda lamarin ya rutsa da su zuwa Babban Asibitin Koko domin samun kulawa, inda wani Sufeto Sa’idu Idiya na SCID ya mutu kamar yadda wani Likita ya tabbatar.

Daga bisani an kai gawar tare da sauran waɗanda abin ya rutsa da su zuwa FMC da ke Birnin Kebbi domin ci gaba da yi musu magani.

Allah ya jikan sufeto Sa’id Idiya ya huta a Jannatul Fiddaus, amin. Tuni dai aka yi jana’izarsa kamar yadda addinin Musulunci ya tanada

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hatsari

Jirgin sojin Najeriya ya faɗo a Kaduna

Published

on

Jirgin sojin Najeriya ya faɗo a Kaduna

Jirgin sojin Najeriya ya faɗo a Kaduna

Wani jirgin sama na sojin Najeriya ya yi hatsari a ƙauyen Tami da ke yankin Karamar Hukumar Igabi a Jihar Kaduna.

Wani mazaunin yankin ya ce jirgin sojin mai sauƙar ungulu ne, kuma ya yi hatsari ne da misalin karfe 5 na asubar Litinin din nan.

Mazauna yankin sun bayyana cewa matukin ya fito daga cikin tarkacen jirgin da ya fado.

Bayan nan sojoji suka yi gaggawar zuwa suka yi wa yankin kawanya tare da fara bincike.

Sojojin sun kuma hana mutane isa wurin da tarkacen jirgin yake.

KU KUMA KARANTA: Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin jirgin samanta

An ce jirgin yana tsaka da aikin sintiri a yankin ne ya samu matsala, lamarin da ya haddasa faduwarsa.

Kawo yanzu Hedikwatar Rundunar Sojin Sama ta Najeriya ba ta fitar da sanarwar game da lamarin ba.

Continue Reading

Hatsari

Wani mummunan hatsari yayi sanadiyyar mutuwar mutane 16 daga cikin 18 da ke motar

Published

on

Wata motar fasinja da ta taso daga Bauchi ta yi hatsari a Inugu kuma mutum 16 daga cikin fasinjoji 18 dake motar maza 14 mata 2 sun mųțtu, wasun su ma ba a iya gane su don sun ƙone ƙurmus.

‘Yan sanda sun ce lamarin ya faru da yammacin jiya Talata, 30 ga watan Afrilu a babban titin garin Ekwegbe.

KU KUMA KARANTA: Fasinjoji sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a Kogi

Motar ƙirar Toyota Hummer Bus ce 18 seater dauke da lambar Bauchi, DAS 215 XA, kuma an rubuta “Masha Allah” a jikin motar.

Don haka Kwamishinan yan sanda na Enugu ke roƙon jama’a duk wanda Allah yasa ya san wani daga cikin fasinjojin to a tuntubi rundunar a 08098880172 ko 08086671202

Continue Reading

Gobara

Mutane da dama sun mutu, sakamakon fashewar tankar mai a Fatakwal

Published

on

Ana fargabar mutane da dama sun rasa rayukansu bayan da wata tankar mai ta kama da wuta a hanyar East-West Road a birnin Fatakwal da ke jihar Rivers a kudancin Najeriya.

Jaridun Punch da na Vanguard sun ruwaito cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 9:45 na daren Juma’a.

Bayanai sun yi nuni da cewa bayan da tankar ta mai ta kama da wuta, ta shafi motoci aƙalla goma da ke jerin cunkoson ababen hawa a birnin na Fatakwal.

KU KUMA KARANTA:Matatar man Fatakwal za ta koma bakin aiki cikin watan Afrilu – Kyari

Wani da ya shaida lamarin ya faɗawa jaridar Vanguard cewa ya ji ƙara har sau biyu masu firgitarwa daga baya kuma hayaƙi ya turnuƙe sararin samaniya.

“Idan kuna da ‘yan’uwa a Fatakwal ku ƙira su don ku ji lafiyarsu” Wani mazaunin birnin na Fatakwal mai suna Bassey Esang Don, ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto ba a san musabbabin fashewar da ta auku ba ko iya sanin adadin mutanen da suka mutu.

Faɗuwar tankar mai ta kama da wuta ba baƙon abu ba ne a Najeriya, inda a wasu lokuta mutane kan yi rububin zuwa kwasar man idan yana Malala.

Daga nan ne kuma akan samu akasi har wuta ta kama ta laƙume rayukan mutane.

Wannan al’amari na faruwa ne yayin da farashin mai ya ƙara tsada a Najeriya inda litar mai ta kusa kai wa Naira 1,000 a sassan ƙasar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like