Connect with us

Ƙasashen Waje

Mohamed Bazoum ya yi yunƙurin tserewa — Sojojin Nijar

Published

on

Sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar sun ce sun daƙile wani yunƙuri da hamɓararren shugaban ƙasar Mohamed Bazoum ya yi na tserewa daga ƙasar.

Sun bayyana haka ne a wata sanarwa da suka karanta a gidan talabijin na ƙasar ranar Alhamis da maraice.

Bazoum yana tsare a hannun sojin da suka kifar da gwamnatinsa ranar 26 ga watan Yuli duk da cewa ƙasashen duniya sun yi ta kiraye-kirayen sakinsa.

Mai magana da yawun gwamnatin sojin Kanar-Manjo Amadou Abdramane, wanda ya bayyana hakan a jawabin da ya yi wa ‘yan ƙasar, ya ce Bazoum da iyalansa da taimakon wasu jami’an tsaro, sun kitsa tserewa ta hanyar tuƙa shi zuwa wajen birnin Yamai babban birnin ƙasar, inda daga nan zai shiga jirgi mai sauƙar ungulu zuwa Nijeriya mai maƙwabtaka.

Ya ƙara da cewa Bazoum ya yi ƙoƙarin tserewa da ƙarfe uku na safiyar ranar Alhamis tare da iyalansa da masu dafa masu abinci biyu da kuma jami’an tsaro guda biyu.

KU KUMA KARANTA: Amurka ta soke tallafin dala miliyan 442 da take ba wa Nijar

“Matakin gaggawa da jami’an tsaro suka ɗauka ya sa sun iya daƙile yunƙurin wanda aka shirya shi don kawo ruɗani a ƙasarmu,” in ji Kanar-Manjo Abdramane.

Sai dai ba a ji martani daga ɓangaren hamɓarar Shugaba Bazoum ba, wanda har yanzu ba a san inda yake ba.

Juyin mulkin da aka yi a Nijar shi ne na biyar a yankin Yammacin Afirka a cikin shekara uku.

Kamar yadda aka hamɓarar da zaɓaɓɓun shugabanni a Mali da Burkina Faso, sojoji sun ce sun hamɓarar da Bazoum ne saboda ci gaba da ƙaruwar rashin tsaro da ya yi sanadin mutuwar dubban mutane a yankin, wanda sojojin suka ce za su iya magancewa fiye da gwamnatin farar hula.

’Yan jam’iyyar Bazoum da iyalansa sun ce an yanke masa ruwa da wutar lantarki, abin da ya jawo Allah-wadai daga ƙasashen yammacin duniya, tsofaffin ƙawayen Nijar.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Published

on

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Daga Ibraheem El-Tafseer

Frane Selak ya kasance wanda ya fi kowa tsallake rijiya da baya a duniya.

A shekarar 1962 ya tsallake haɗarin jirgin ƙasa wanda mutane 17 suka mutu, a 1963 jirgi ya faɗi da shi kowa ya mutu sai shi kaɗai ko ƙwarzane bai yi ba.

A shekarar 1966 motar safa ta lume da su a rafi mutum huɗu sun mutu amma Frane bai samu ko ƙwarzane ba a yayin da a shekarar 1973 motarsa ta kama da wuta ya tsallake rijiya da baya, ya kuma tsallake haɗarin taho mu gama da mota ta yi da shi ya tsira ya kuma lashe yuro dubu ɗari takwas a Caca a shekarar 2003.

KU KUMA KARANTA: Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Published

on

Isra'ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza, inda ta tilasta wa ɗaruruwan Falasɗinawa tserewa bayan da soji suka kuma ba da umarnin ƙaurace wasu yankuna masu yawan jama’a.

KU KUMA KARANTA: Sojojin Isra’ila sun ce an yi musayar wuta da dakarun Masar

Waɗanda suka shaida lamarin sun ce an kai hari da dama a ciki da wajen birnin Khan Younis, inda aka hallaka mutane takwas kuma mutane sama da 30 suka samu raunuka, cewar wata majiyar lafiya da kuma ƙungiyar Red Crescent ta Falasɗinawa.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC

Published

on

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana - COPEC

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC

Ƙungiyar Kare Haƙƙin Masu Amfani da Man Fetur a Ghana ta yi hasashen cewa akwai yiwuwar a samun ƙarin farashin man fetur a ƙasar a farkon watan Yulin 2024.

Ƙungiyar ta Chamber for Petroleum Consumers (COPEC) ta ce akwai alamu masu ƙarfi da ke nuna cewa farashin fetur da man dizel da gas zai ƙaru baki ɗaya a gidajen man da ke faɗin ƙasar, kamar yadda kamfanin watsa labarai na ƙasar Ghana ya ruwaito.

COPEC ɗin ta ce za a samu ƙarin farashin ne sakamakon yadda farashin Cedi ɗin a ƙasar ke ƙara karewa idan aka kwatanta da dalar Amurka.

COPEC ɗin ta yi hasashen cewa farashin man fetur ɗin wanda za a rinƙa sayarwa a gidan mai zai ƙaru da kashi 2.17 cikin 100, wanda hakan ke nufin zai ƙaru daga Cedi 14.17 zuwa Cedi 15.20 a duk lita.

Sai kuma farashin dizel ana sa ran ya ƙaru zuwa 15.21 a kowace lita ɗaya, sai kuma na gas ya koma tsakanin Cedi 13.24 zuwa Cedi 14.64 a duk kilo ɗaya.

KU KUMA KARANTA: Ɗan Ghana ya kafa tarihi na rungumar bishiyoyi a duniya

Ƙungiyar ta COPEC ta bayar da shawara ga gwamnatin Ghana da ta yi duk mai yiwuwa domin rage harajin da yake a kan gas ko kuma yin tallafi a farashinsa domin bayar da dama ga ‘yan ƙasar su same shi a farashi mai rahusa.

Ta kuma yi ƙira ga gwamnati da kada ta yi ƙasa a gwiwa wajen dawo da matatar mai ta Tema a kan aiki (TOR) don kaucewa ko kuma rage shigo tattacen man fetur wanda a wani lokacin ake samun gurɓatacce.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like