Ƙasashen Waje
Ministan Wajen Turkiyya ya yi gargaɗi kan yiwuwar ɓarkewar rikici, saboda harin da Amurka ke kai wa ƙungiyoyin da Iran ke goyon baya
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/02/Screenshot_20240205-092541_1.jpg)
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Hakan Fidan ya yi gargaɗi game da yiwuwar watsuwar rikici a Gabas ta Tsakiya a yayin da Amurka ke matsa ƙaimi wurin kai hare-hare kan ƙungiyoyin da Iran take goyon baya.
“Idan kana wasa da wuta, mai yiwuwar wutar ta zama tamkar gobara wadda ba za a iya shawo kanta ba. Muna fuskantar hatsari, kuma akwai babbar barazana ta yiwuwar gaza shawo kan abin da zai faru,” a cewar Fidan a wata hira da gidan talbijin na ƙasa ranar Lahadi.
Fidan ya ce Turkiyya tana tattaunawa da Amurka da sauran ƙasashen da ke yankin a-kai-a-kai , yana mai ƙarawa da cewa: “Akwai buƙatar mu guje wa watsuwar rikicin zuwa wasu sassan yankin. Halin da ake ciki ba mai kyau ba ne. Za mu iya fuskantar watsuwar rikicin sosai.”
KU KUMA KARANTA: Turkiyya za ta ci gaba da fallasa farfagandar Isra’ila – Altun
Da yake magana game da masu bijiro da batun tsaron Isra’ila a koyaushe, Fidan ya ce babban abin da Isra’ila ta sanya a gaba shi ne fadada iyakokinta maimakon tsaronta.
Isra’ila za ta samu zaman lafiya ne idan ta daina “shirga karga” ga ƙasashen duniya sannan ta bari Falasɗinawa suka samu kasa mai ƴancin kanta, a cewar ministan harkokin wajen na turkiyya.
Fidan ya jaddada tunatarwa ga kasashen yankin waɗanda suka sha alwashin cewa a shirye suke su ɗauki nauyin tabbatar da zaman lafiya, inda ya ce: “Lokacin da muka bijiro da batun samar da ƙasashe biyu masu ƴancin kansu, babban burinmu shi ne mu kasance masu shiga tsakani wajen tabbatar da hakana.”
Ƙasashen Waje
Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali
![Harin ta'addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/IMG_20240704_074342.jpg)
Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali
Wani hari da ake kyautata zaton masu ikirarin jihadi ne suka kai ƙauyen Djiguibombo da ke kusa da garin Bandiagara a yankin tsakiyar ƙasar Mali, ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20, kamar yadda wasu hukumomin yankin biyu suka tabbatar.
Majiyoyin da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da mutuwar mutane 20, sannan suka ce yadda lamuran tsaro suka taɓarɓare a yankin, ya hana jami’an tsaro kai ɗauki wajen.
Wani jagoran matasan yankin shi ma da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce tun a farkon daren ranar Litinin ɗin data gabata ne maharan suka kai farmakin, inda suka kwashe tsawon sa’oi uku a cikin garin.
KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe ‘yan jarida 106 a yakin da take yi a Gaza — Jami’ai
Ya ce sama da mutane 20 ne aka kashe a harin, kuma fiye da rabinsu matasa ne inda aka ranke musu harsuna.
Kasar Mali dai na fama da matsalolin tsaro na ƙungiyar Al-Qaeda da kuma na IS tun a shekarar 2012, inda ya bazu kasashen Burkina Faso da Nijar da ke makwabtaka da ita.
Tun bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi a kasar a shekarar 2020, hukumomi ke jin tsoron fitowa fili su sanar da labarin hare-haren ta’addancin da ake kai wa kasar da ke Yammacin Afrika.
Ƙasashen Waje
A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila
![A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama - Ministan Tsaron Isra'ila](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/20243475_0-0-5499-3097.jpeg)
A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila
Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce sojojin Isra’ila za su kasance a shirye don daukar duk wani matakin da ya dace kan ƙungiyar Hizbullah ta ƙasar Labanon, ko da yake abin da ake so shi ne cimma matsaya ta shawarwari.
Muna kai wa ƙungiyar Hizbullah hari sosai a kowace rana kuma za mu kai ga cikakken shiri na ɗaukar duk wani mataki da ake buƙata a ƙasar Labanon, ko kuma cimma wani shiri daga matsayi mai ƙarfi.
KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan
Mun fi son tsari, amma idan aka kai mu maƙura za mu san yadda za mu yi yaƙi,” an ruwaito Gallant a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.
Ƙasashen Waje
Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan
![Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/20306309_0-402-5000-2817.jpeg)
Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan
Aƙalla mutum 12 ne suka mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a jiya Laraba a wani hari da aka kai kan wata kasuwar dabbobi da ke El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Yammacin Sudan.
A wata sanarwa da kwamitin sulhu na kwamitocin ‘yan gwagwarmaya na El Fasher ya fitar ya ce “harbin bindigogi a kasuwar dabbobi da ke birnin El Fasher ya yi sanadin mutuwar fararen hula 12 da kuma wasu 20 da suka samu raunuka daban-daban.”
Tun da fari a ranar Larabar da safe, kwamitocin ‘yan gwagwarmaya sun ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai mummunan hari El Fasher da manyan bindigogi.
Tun a ranar 10 ga Mayu, aka fara ƙazamin fada tsakanin sojojin Sudan da RSF a El Fasher. Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa ke amfani da birnin a matsayin cibiyar ayyukan jinƙai ga yankin Darfur.
Rikicin Sudan ya ɓarke ne a cikin watan Afrilun 2023 tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo kan yarjejeniyar shigar da RSF cikin rundunar soja.
KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD
Ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 16,000, da raba kusan mutum miliyan 10 da muhallansu, sannan sama da miliyan 25 na buƙatar agajin jinƙai, lamarin da ya zama mafi girma a duniya ta ɓangaren matsalar rashin matsuguni da yunwa, a cewar MƊD.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai9 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano