No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wani magidanci ya hallaka matarsa saboda taliyar yara a yankin Olota da ke ƙaramar hukumar Alimosho a Jihar Legas.

Ana zargin magidancin ya yi wannan aika-aika ne bayan da ya dawo daga aiki ya samu matarsa ta dafa taliyar yara maimakon abincin da ya fi so.

Wata majiya da ta buƙaci a sakaya sunanta saboda tsaro, ta ce mijin ya bar matar kwance bayan ya doke ta da dutse a kanta.

Majiyar ta ce wani makwabcin magidancin ne ya ƙira magidancin ya sanar da shi matarsa na cikin wani yanayi.

Makabtan ne suka garzaya da matar zuwa asibiti inda a can ne aka tabbatar da rasuwarta.

KU KUMA KARANTA: Wani matashi ya kashe mahaifiyarsa

Shaidu sun ce ’yan sanda sun cafke miji inda suna gudanar da bincike domin gano hakikanin abin da ya faru a tsakaninsa da matarsa.

Amma rundunar ’yan sandan jihar Legas ta ce kawo yanzu ba a tabbatar da cewar mijin ne ya kashe matar ba.

Kakakin rundunar, Benjamin Hundeyin ya ce suna kan bincike kuma da zarar sun kammala za su bayyana wa jama’a sakamakon binciken da suka samu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...