No menu items!

Sample Page Title

Date:

Dubun wani matashi mai shekara 37 ta cika bayan da ya yi wa wata tsohuwa ’yar shekara 62 fyaɗe a Jihar Borno.

Matashin wanda yanzu haka yake komar ’yan sanda ya kuma sace wa dattijuwar kuɗi, bayan da ya yi mata fyaden a ƙauyen Panshani, gundumar Gasi da ke ƙaramar Hukumar Shani ta jihar.

An kama wanda ake zargin ne bayan ɗan uwan dattijuwar ya kai ƙara wurin ’yan sanda cewa tsohuwar mai shekara 62 na komawa gida daga unguwa ne matashin ya tare ta a hanya “ya yi mata fyaɗe, ya kwashi kuɗi naira dubu arba’in da biyu da ɗari bakwai a aljihunta.

KU KUMA KARANTA: Yadda mutum huɗu suka yi wa Yarinya fyade saboda laifin babanta

“Don haka yanzu haka ana ci gaba da bincike, kuma da zarar an kammala za a miƙa shi gaban ƙuliya don fuskantar hukuncin da ya yi dai-dai da shi,” in ji Kwamishinan ’yan sandan jihar, Muhammad Yusufu.

Ya ƙara da cewa a cikin watanni ukun da suka gabata rundunar ta kama mutane aƙalla 500 kan aikata laifuka daban-daban a sassan jihar, kuma yawancinsu an miƙa su gaban ƙuliya.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...