Connect with us

Al'ajabi

Matashi ɗan shekara 17 ya kashe kansa a Bauchi

Published

on

Wani matashi ɗan shekara 17 mai suna Master Betwom Bitrus mazaunin Bombar da ke ƙaramar hukumar Ɓogoro a jihar Bauchi, an zargi shi da kashe kansa.

Jami’in ‘yan sanda mai kula da yankin Mista Simon Vandi ne ya tabbatar wa manema labarai wannan mummunan lamari, inda ya bayyana cewa lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata.

A cewar rahoton ‘yan sanda, marigayi Betwom, tare da abokansa, ya je rafin Bombar zuwa yin wanka da yammacin Talata kafin lamarin ya faru.

An ruwaito DPO ɗin yana cewa, “Ina tabbatar muku da misalin ƙarfe 12 na daren yau (Laraba), ofishina ya samu rahoton kashe kansa da wani matashi mai suna Master Betwom Bitrus ɗan shekara 17, mazaunin Bombar a nan garin Ɓogoro ya yi. ”

Ya ƙara da cewa, “Bincike ya nuna cewa yana tare da abokansa jiya (Talata), da yamma. Babu wanda ya san dalilin da ya sa ya rataye kansa.

KU KUMA KARANTA: DSS sun cafke matashin malamin nan Malam Baffa Hotoro a jihar Kano

An tsinci gawarsa a jikin bishiyar da ya rataye kansa. An kai shi babban asibiti inda aka tabbatar da rasuwarsa.”

DPO ya ci gaba da cewa, har yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike domin gano dalilin da ya haddasa faruwar lamarin, inda ya ce, “Na yi nadamar rasuwar marigayi Betwom Bitrus, kuma ina baƙin ciki da iyalan mamacin.”

Da yake magana kan lamarin, wani mazaunin Bombar, Mista Daniel Haruna ya ce, “Eh, ina so in gaya muku cewa wani matashi ya kashe kansa kuma ba mu san dalilin da ya sa ba.

Muna cikin baƙin ciki a halin yanzu. An gan shi na ƙarshe tare da abokansa jiya (Laraba) da yamma.

Ana ci gaba da ƙoƙarin samun muhimman bayanai daga abokanan da aka gan shi a ƙarshe domin a tabbatar da abin da ya kai ga aukuwar lamarin kamar yadda wata sanarwa da Gomna James, jami’in yaɗa labarai ya fitar.

2 Comments

2 Comments

  1. Pingback: Ya kashe ‘yar da aka haifa masa, a kan ya fi son ɗa namiji | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Ɗalibin sakandare a Benuwe ya kashe kansa | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Al'ajabi

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Published

on

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano a arewacin Najeriya ta ce ta kama wani mutum da ake zargi da cinna wa wani masallaci wuta yayin da mutane ke Sallar Asuba ranar Laraba.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Gadan da ke Ƙaramar Hukumar Gezawa a jihar ta Kano, da misalin karfe 5:20 lokacin da ake sallah, a cewar sanarwa ‘yan sanda.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar wa da TRT Afrika Hausa faruwar lamarin da kama mutumin da ake zargi, sai dai ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike.

Abdullahi Kiyawa ya ce bincike ya nuna cewa mutumin da ake zargi da cinna wutar Shafi’u Abubakar mai kimanin shekaru 38 ya jefa wata roba ne ɗauke da fetur cikin masallacin, sannan ya cinna wuta.

KU KUMA KARANTA: Mahara a Anambara sun ƙona fadar babban Basarake ƙurmus

Kakakin ‘yan sandan ya ce mutum 24 ne suka ƙone a masallacin, da suka haɗar da manya 20, yara huɗu.

An garzaya da duka waɗanda suka jikkata zuwa asibiti don ba su kulawa, amma babu wanda ya mutu a haɗarin, a cewar sanarwar ‘yan sandan.

Continue Reading

Al'ajabi

An tsinci gawar wata ɗaliba a cikin ɗaki a Kano

Published

on

An tsinci gawar wata ɗaliba mai suna Aisha Yahaya ta Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Ɗangote da ke Wudil, a wani gida da ke wajen jami’ar.

Aisha, ɗaliba ce da ke matakin karatu na uku wato ‘level 300’ a sashen nazarin Kimiyya da Fasahar Abinci na jami’ar wadda aka tsinci gawarta bayan ta koma ɗakinta.

An ce ɗalibar ta rubuta jarrabawarta ta farko a zangon karatun na farko da ake yi a jami’ar.

Wasu daga cikin abokan karatunta sun danganta mutuwarta da shiga cikin matsi da damuwa a dalilin karatu da kuma zana jarrabawar.

A cikin wasiƙar ta’aziyyar, hukumar jami’ar ta bayyana matuƙar baƙin cikinta dangane da rasuwar Aisha Yahaya.

KU KUMA KARANTA: An tsinci gawar wani mutum a kan titi a Kano

Sanarwar ta ce, “Aisha ɗaliba ce mai hazaƙa wadda ta rasu a dalilin bugun zuciya. Za a riƙa tunawa da ita a kan sha’awarta na karatu da jajircewarta kan harkokin karatunta.”

Jami’ar ta ƙara da cewa, ba a iya gano wata da ke tattare da ita ba gabanin mutuwarta saboda ba ta nuna alamun rashin lafiya ko fama da wata cuta ba.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like