Connect with us

Labarai

Matakan da Limaman Jihar Neja suka ɗauka kan auren marayu 100 da Ministar Mata ke inkari

Published

on

Matakan da Limaman Jihar Neja suka ɗauka kan auren marayu 100 da Ministar Mata ke inkari

Limaman Masallatan Juma’a na Jihar Neja da Kwamitin Malamai da iyayen yara 100 da gwamnati ke son aurar da su, sun ce sun ɗauki matakan da suka ga sun dace na tabbatar da yiwuwar aurarrakin, wanda Ministar Mata ta Najeriya ke ƙalubalanta.

A wata sanarwa da daraktan da ke kula da harkokin addini na jihar ya fitar a yau Juma’a, ta ce masu ruwa da tsakin sun yi taron ne a Minna, inda suka tattauna kan batun umarnin kotu da kuma ƙarar Shugaban Majalisar Dokokin jihar Barista Abdulmalik Sarkin Daji da Ministar Matan ta shigar, kan batun ɗaukar nauyin auren marayu 100 da aka shirya yi a ƙaramar hukumar Mariga.

Batun aurar da ‘yan matan ya jawo ce-ce-ku-ce sosai a Najeriya, wanda Minsitar Matan Uju Kennedy-Ohanenye ta shigar da ƙara kotu don neman a dakatar da yin sa a ranar 24 ga watan Mayu kamar yadda aka tsara tun da farko.

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin Kano ta sa hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

A ganin Ministar, ‘yan matan waɗanda yawanci marayu ne da suka rasa mahaifansu a hare-haren ‘yan bindiga da ya addabi jihar, “wani abu daban suka cancanci a yi musu.” kuma ma’aikatarta na bincike don gano ko su wane ne ‘yan matan 100 da shekarunsu da kuma ko bisa amincewarsy za a yi auren.

Sai dai ko a ranar Juma’a, Minista Uju ta wallafa a shafinta na X cewa ta cimma matsaya tare da Sarkin Kotangora, HRH Alh Mohammed Barau Muazu da Kakakin Majalisar Abdumalik Sarkindaji, kan neman hanyar hadin gwiwa don bai wa ‘yan matan sabuwar rayuwa, amma har yanzu hukuncin Kotun yana nan ba kawar da shi ba.

“Ban janye shari’ata ba har sai mun gudanar da aikin tantance ‘yan matan, sannan za mu sa ‘yan matan su shiga makarantu, da koyar da sana’o’in hannu da kuma karfafa wa ‘ya’ya mata, babban burin ma’aikatarmu shi ne tabbatar da ganin an samar da walwala kuma an tabbatar da bukatun ‘yan matan”.

Sanarwar daraktan harkokin addinan ta ce matakai biyar Limamai da Malamai da Iyayen yaran suka ɗauka kan wannan lamari kamar haka;
1. Za a ɗaura auren marayu 100 a ranar 24 ga Mayu, 2024 kamar yadda aka tsara. Dalili shi ne, babu ta inda auren da aka shirya yi ya saɓa wa kundin tsarin mulkin ƙasa da kuma dokokin addininMusulunci.

2. Mahalarta taron sun buƙaci Ministar Harkokin Mata Mrs. Uju ta nemi afuwar jama’a nan da kwana bakwai ko kuma a dauki matakin shari’a a kanta.

3. Taron ya yi ƙira ga Shugaban Najeriya da ya kori Ministar cikin gaggawa domin kauce wa rikicin addini a ƙasar.

4. Taron ya kuma yi ƙira ga ɗaiɗaikun jama’a da ‘yan siyasa da su yi koyi da shugaban Majalisar Dokokin kan irin wannan halayya.

5. A karshe taron ya yi ƙira ga al’ummar Musulman jihar da su ci gaba da kasancewa masu bin doka da oda domin malamai da shugabannin addinin Musulunci na kan gaba a lamarin.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

Labarai

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Published

on

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

A ƙoƙarinsa na kauce wa rikicin manoma da makiyaya da ke yawan faruwa a lokacin damuna, Shugaban Karamar Hukumar Kwami a Jihar Gombe, Dakta Ahmed Wali Doho, ya kafa kwamitin tsaro da sanya ido kan ɓangarorin.

Da yake zantawa da manema labarai a ofishinsa da ke garin Malam Sidi, shugaban karamar hukumar, ya bukaci manoma da su guji noma burtalolin shanu, wanda hakan ke haifar da rikici tsakaninsu da makiyaya, da ke haifar da asarar rayuka.

Su ma makiyayan ya gargade su da cewa su guji shiga gonakin manoma, saboda hakan ne ke jawo rikici idan suka cinye musu amfanin gona.

A cewarsa, lokacin girbi me aka fi samun rikicin manoma da makiyayan, saboda haka kwamitin zai ci gaba da sa ido daga yanzu har zuwa lokacin girbin don ganin ba a samu rikici ba.

KU KUMA KARANTA: Gwamna Yusuf ya amince da sayen taki na naira biliyan 5 don manoman Kano

Ya ƙara da cewa, kusancin garin Kwami da rafi ya sa ya zama wuri mai kyau don noman rani.

Don haka ya ja hankalin manoman yankin da su yi amfani da wannan damar wajen bunkasa tattalin arzikinsu.

Ya jaddada cewa noman rani na da matukar muhimmanci wajen magance matsalar karancin abinci a Najeriya.

Hakan ne ya sa suka haɗa kan matasan yankin don su fara noman rogo da zai taimaka wajen shawo kan matsalar ƙarancin abinci da rage wa manoma tsadar takin zamani.

Continue Reading

Labarai

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Published

on

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da ɓata-garin cikin

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da bata-gari a cikinsu.

Kwamishin ’yan sandan jihar, Garba Ahmed, ya sanar da shirin bayan an kama wasu ’yan banga uku da aikata manyan laifuka.

Ya jaddada muhimmancin sake duba ayyukan ’yan banga a jihar, duk da  muhimmiyar rawar da suke takawa wajen taimaka wa jami’an tsaro a yaki da miyagun laifuka.

Ya ce yin gyaran da kuma tantancewa ya zama dole sakamakon ƙorafe-ƙorafen neman yin hakan daga jama’a.

Ya bayyana cewa jama’a sun yi ƙiran ne bayan kama wasu ’yan banga uku da laifin hada baki wajen shiga gida, sata, ƙwace da kuma sayar da kayan sata a Damaturu.

Wata sanarwa da DSP Dungus Abdul Karim, kakakin rundunar, ya fitar, ta ce wasu daga cikin ’yan banga sun kai korafi bayan faruwar lamarin.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun kashe mutum 12 a Kaduna, sun kai hari a ofishin ƴan sanda a Zamfara

“A ranar 27 ga watan Yuni, 2024, rundunar ta amsa kiran wani mai shago a Damaturu, wanda ya dauki ’yan banga aikin gadi, amma suka kwashe kayan shagon na makudan kudade ba tare da bayani ba.

“Bincike ya kai ga kama wasu mutane biyu da kayan sata da ake zargin sun saya ne daga wani dan banga wanda nan take aka kama shi.

“Ana shawarta jama’a da su yi taka-tsan-tsan wajen daukar masu gadi, sannan su kai rahoton ’yan banga da aka ga suna aikata laifi a bakin aikinsu.”
Sanarwar ta ci gaba da cewa, rundunar tana ɓullo da tsare-tsare don daukar bayanan ’yan banga domin sa ido kan ayyukansu.

Ta ci gaba da cewa ofisoshin ’yan sanda na yankuna da ke jihar za su jagoranci wannan aikin tantancewan domin kawar da baragurbi a cikin ’yan banga.

“Don  haka ake ƙira ga jama’a da su ci gaba da tallafa wa ’yan sanda wajen jainrahoton ayyukan jami’an tsaron da ba su dace ba a hedkwatar jihar ta lamba 07068858500, ko kuma a gabatar da wasikar korafin ga kwamishinan ’yan sanda  ta hanyar kakakin rundunar,” in ji sanarwar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like