Connect with us

Labarai

Matakan da Limaman Jihar Neja suka ɗauka kan auren marayu 100 da Ministar Mata ke inkari

Published

on

Matakan da Limaman Jihar Neja suka ɗauka kan auren marayu 100 da Ministar Mata ke inkari

Limaman Masallatan Juma’a na Jihar Neja da Kwamitin Malamai da iyayen yara 100 da gwamnati ke son aurar da su, sun ce sun ɗauki matakan da suka ga sun dace na tabbatar da yiwuwar aurarrakin, wanda Ministar Mata ta Najeriya ke ƙalubalanta.

A wata sanarwa da daraktan da ke kula da harkokin addini na jihar ya fitar a yau Juma’a, ta ce masu ruwa da tsakin sun yi taron ne a Minna, inda suka tattauna kan batun umarnin kotu da kuma ƙarar Shugaban Majalisar Dokokin jihar Barista Abdulmalik Sarkin Daji da Ministar Matan ta shigar, kan batun ɗaukar nauyin auren marayu 100 da aka shirya yi a ƙaramar hukumar Mariga.

Batun aurar da ‘yan matan ya jawo ce-ce-ku-ce sosai a Najeriya, wanda Minsitar Matan Uju Kennedy-Ohanenye ta shigar da ƙara kotu don neman a dakatar da yin sa a ranar 24 ga watan Mayu kamar yadda aka tsara tun da farko.

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin Kano ta sa hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

A ganin Ministar, ‘yan matan waɗanda yawanci marayu ne da suka rasa mahaifansu a hare-haren ‘yan bindiga da ya addabi jihar, “wani abu daban suka cancanci a yi musu.” kuma ma’aikatarta na bincike don gano ko su wane ne ‘yan matan 100 da shekarunsu da kuma ko bisa amincewarsy za a yi auren.

Sai dai ko a ranar Juma’a, Minista Uju ta wallafa a shafinta na X cewa ta cimma matsaya tare da Sarkin Kotangora, HRH Alh Mohammed Barau Muazu da Kakakin Majalisar Abdumalik Sarkindaji, kan neman hanyar hadin gwiwa don bai wa ‘yan matan sabuwar rayuwa, amma har yanzu hukuncin Kotun yana nan ba kawar da shi ba.

“Ban janye shari’ata ba har sai mun gudanar da aikin tantance ‘yan matan, sannan za mu sa ‘yan matan su shiga makarantu, da koyar da sana’o’in hannu da kuma karfafa wa ‘ya’ya mata, babban burin ma’aikatarmu shi ne tabbatar da ganin an samar da walwala kuma an tabbatar da bukatun ‘yan matan”.

Sanarwar daraktan harkokin addinan ta ce matakai biyar Limamai da Malamai da Iyayen yaran suka ɗauka kan wannan lamari kamar haka;
1. Za a ɗaura auren marayu 100 a ranar 24 ga Mayu, 2024 kamar yadda aka tsara. Dalili shi ne, babu ta inda auren da aka shirya yi ya saɓa wa kundin tsarin mulkin ƙasa da kuma dokokin addininMusulunci.

2. Mahalarta taron sun buƙaci Ministar Harkokin Mata Mrs. Uju ta nemi afuwar jama’a nan da kwana bakwai ko kuma a dauki matakin shari’a a kanta.

3. Taron ya yi ƙira ga Shugaban Najeriya da ya kori Ministar cikin gaggawa domin kauce wa rikicin addini a ƙasar.

4. Taron ya kuma yi ƙira ga ɗaiɗaikun jama’a da ‘yan siyasa da su yi koyi da shugaban Majalisar Dokokin kan irin wannan halayya.

5. A karshe taron ya yi ƙira ga al’ummar Musulman jihar da su ci gaba da kasancewa masu bin doka da oda domin malamai da shugabannin addinin Musulunci na kan gaba a lamarin.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Tinubu ya naɗa sabbin sakatarorin dindindin

Published

on

Tinubu ya naɗa sabbin sakatarorin dindindin

 

Tinubu ya naɗa sabbin sakatarorin dindindin

Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya amince da naɗin sabbin sakatarorin dindindin na gwamnatin tarayya guda takwas da za su cike guraben da ake da su a wasu jihohi da shiyyoyin ƙasar a ma’aikatan gwamnati.

Ajuri Ngelale, mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai da bayanai ne ya bayyana hakan a wata sanarwa a jiya Juma’a, inda ya ce an naɗa sabbin sakatarorin dindindin ɗin ne bayan da ofishin shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayya ya gudanar da aikin zaɓo su.

KU KUMA KARANTA:Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3

Sakatarorin su ne: Dr Emanso Umobong Okop – Akwa-Ibom, Obi Emeka Vitalis – Anambra, Mahmood Fatima Sugra Tabi’a – Bauchi, Danjuma Mohammed Sanusi – Jigawa, Olusanya Olubunmi – Ondo, Dr Keshinro Maryam Ismaila – Zamfara, Akujobi Chinyere Ijeoma (Kudu-maso-Gabas)) da kuma Isokpunwu Christopher Osaruwamwen (Kudu-maso-Kudu).

“Shugaban ya yi hasashen cewa sabbin sakatarorin dindindin na gwamnatin tarayya za su yi aiki da ƙwazo, himma da riƙon amana ga ƙasa wajen gudanar da ayyukansu tare da tabbatar da ingantacciyar hidima ga al’ummar Najeriya,” in ji sanarwar.

Continue Reading

Labarai

Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3

Published

on

Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3

 

Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da ba da Naira dubu hamsin-hamsin ga iyalai miliyan 3.6 har tsawon wata uku a faɗin Nijeriya.

Wannan na ɗaya daga cikin yarjejeniyoyi da aka cimma a ganawar da Tinubu ya yi da gwamnonin jihohi 36 na ƙasar nan a yau Alhamis a Abuja.

Shugaban ya ba da umarnin raba kuɗin ga iyalai dubu 100 a kowace jiha har na tsawon watanni uku.

Sauran batutuwa da aka cimma a ganawar sun haɗa da:

* Bawa iyalai 100,000 a kowace jiha tallafin N50,000 na tsahon wata uku.

* Ware Naira biliyan 155 domin siyen kayan abinci da za a tallafawa masu ƙaramin ƙarfi kan farashi mai rahusa.

* Baiwa kowace jiha Naira biliyan 10 domin sayen motocin sufuri masu aiki da iska gas domin sauko da farashin kuɗin zirga-zirga.

KU KUMA KARANTA:Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa

* Gaggauta fara aikin hanyar da ta tashi daga Sakkwato zuwa Badagary a Lagos. Hanyar zata ratsa ƙauyuka kimanin 216, madatsun ruwa (dams) guda 58, ƙananan hukumomi 156 da manyan garuruwa 39 da kuma gonaki da suka kai kimanin hectare miliyan ɗaya. Titin zai ratsa jihohin Sokoto da Kebbi da Niger da Kwara da Oyo da Ogun da kuma Lagos.

* Shugaba Tinubu ya kuma amince da biyan kuɗin aikin hanyar jirgin ƙasa daga Fatakwal zuwa Maiduguri wadda za ta ratsa jihohin Rivers da Abia da Enugu da Benue da Nasarawa da Plateau da Bauchi da Gombe da Yobe da kuma Borno.

* Haka nan an amince da biyan kuɗin da ake buƙatar domin yin aikin hanyar jirgin ƙasa da ta taso daga Ibadan zuwa Abuja a wani ɓangare na aikin dogo da ya tashi daga Lagos zuwa Kano. Aikin zai haɗa jihohin Lagos da Ogun da Oyo da Osun da Kwara da Niger da Abuja da Kaduna da kuma Kano.

* Shugaban ƙasa ya kuma bada umarnin cigaba da aikin hanyar Lagos zuwa Calabar wadda kuma zata yi rassa a jihohin Benue da Kogi da Abuja da Nasarawa da Enugu da Ebonyi.

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Kano ta mayar da martani kan ɗaga tuta a fadar Nasarawa

Published

on

Gwamnatin Kano ta mayar da martani kan ɗaga tuta a fadar Nasarawa

Gwamnatin Kano ta mayar da martani kan ɗaga tuta a fadar Nasarawa

Gwamnatin jihar Kano ta yi watsi da batun ɗaga tutar masarauta da aka yi a gidan sarki na Nassarawa wurin da Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ke zaune, inda ta bayyana hakan da ƙoƙarin jan hankalin jama’a kawai.

Tutar, wata alama ce ta iko dake nuni da cewar Sarki na nan, a kullum ana ɗaga ta da misalin ƙarfe 6 na safe a kuma sauƙe ta da misalin ƙarfe 6 na yamma. Duk lokacin da sarki ba ya cikin fada ko ya yi balaguro za ta kasance a sauƙe.

Da safiyar ranar Alhamis, aka lura cewar an ɗaga tutar da misalin ƙarfe 6 na safiya a fadar Nassarawa, abin da ya haifar da kace-nace dama raɗe-raɗi.

Kowane daga cikin Aminu Ado Bayero da Muhammadu Sanusi II na iƙirarin shi ne Sarkin Kano kuma suna ci gaba da aiwatar da ayyukan sarauta.

KU KUMA KARANTA:An sauya Kwamishinan ’yan sandan Kano

Gwamnatin jihar ce ta sauƙe Aminu Ado Bayero tare da sake naɗa Muhammadu Sanusi biyo bayan yiwa dokar masarautu ta Kano kwaskwarima.

An ɗaga irin wannan tuta a fadar gidan Rumfa, inda Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ke zaune.

Mai magana da yawun gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ne ya yi fatali da batun ɗaga tuta a fadar Nassarawar, inda yace hakan wani yunƙuri ne na jan hankalin al’umma.

Ya shaidawa manema labarai cewar, “hakan wani yunƙuri ne na jan hankalin al’umma. Amma babu shakku ko tantamar cewar Sanusi ne Sarkin Kano.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like