No menu items!

Sample Page Title

Date:

Mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima ya gargaɗi PENGASSAN akan Ɗangote

Daga Jameel Lawan Yakasai

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya bayyana cewa Gwamnatin Najeriya ta fi ƙarfi da tasiri fiye da ƙungiyar ma’aikatan mai ta PENGASSAN.

Yana mai cewa wajibi ne gwamnati ta kare Alhaji Aliko Dangote domin ci gaban tattalin arzikin ƙasa.

Shettima ya ce Dangote ba kawai ɗan kasuwa ba ne, ginshiƙi ne na tattalin arzikin Najeriya wanda ya sadaukar da jarinsa da iliminsa domin bunƙasa ƙasar, don haka irin wannan ɗan ƙasa mai kishin ƙasa yana buƙatar tallafi, ba ƙalubale ba.

KU KUMA KARANTA: Ba za mu sayi man fetur kai tsaye daga Ɗangote ba – Dillalan Man Fetur

Ya ƙara da cewa gwamnati za ta ci gaba da tsayawa tsayin daka wajen kare kamfanonin da ke taimakawa wajen samar da ayyukan yi, rage talauci da ƙarfafa masana’antu a cikin gida.

A cewar sa, irin yadda ake mu’amala da Dangote shi ne ainihin yadda duniya ke kallon martabar Najeriya, don haka babu dalilin barin sa cikin rikice-rikicen siyasa ko matsin ƙungiyoyi.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...