No menu items!

Sample Page Title

Date:

Masu Haƙar ƙaburbura sun koka kan ƙarancin alawus da matsalolin maƙabarta a Kano

Daga Jamilu Lawan Yakasai

Masu haƙa ƙaburbura da gyara maƙabarta a Kano sun koka kan ƙarancin alawus ɗin da ake ba su, wanda ya ragu daga N5,000 zuwa N3,000 ko ma ƙasa da haka a wasu lokuta.

Malam Suleiman Mohammed, wani mai haƙar kabari a maƙabartar Tudun Wada, ya bayyana cewa a wasu lokutan ana shafe watanni ba tare da an biya su ba. Ya ce sun kai ƙorafinsu gaban Sarkin Kano, inda aka yi musu alƙawarin duba lamarin.

KU KUMA KARANTA:Matsalar Ruwa Sha: Yaushe dokar ta-ɓacin Gwamnatin Kano za ta fara aiki? ‎

A cewarsa, aikin haƙa kabari yana da hatsari kuma yana da buƙatar ƙarfi, don haka yana da kyau a inganta alawus ɗinsu. Bugu da ƙari, ya koka kan yadda ɓata gari ke amfani da maƙabarta wajen shaye-shaye da adana makamai kamar yanda ya shidawa wakilin Jaridar Neptune Prime.

Ya nemi a inganta ayyukansu ta hanyar tsaftace maƙabartar da gyara katangarta da sanya fitulu.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...