No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara ta tabbatar da kashe mutum ɗaya tare da yin garkuwa da wasu mutane uku da wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton masu garkuwa da mutane ne.

Kakakin rundunar, Ajayi Okasanmi, ya ce lamarin ya faru ne a ranar 16 ga watan Mayu a Ijara-Isin, cikin ƙaramar hukumar Isin.

An tura jami’an Mista Okasanmi zuwa yankin domin ceto waɗanda lamarin ya shafa tare da kamo waɗanda ake zargin.

Wata majiya da ta nemi a sakaya sunanta, ta bayyana sunan mamacin da Adeyemi na Pamo Isin.

Ya shawarci jama’a da su kasance masu lura da tsaro da kuma kai rahoton duk wani motsi da ake zargin ana kai wa jami’an tsaro domin hana afkuwar rikici.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

2 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...