No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Shafa’atu Dauda, Kano

A ranar Jumu’a da misalin ƙarfe 10:00 na dare wasu ɓata-garin masu ƙwacen waya da ke yawo a babur suka tare Musa Sani Aliyu (Khan) tare da nufin karɓan wayar dake aljihunsa.

A lokacin Musa ya fito daga wurin aikinsa Jalla Radio da nufin tsare abin hawa zuwa gida.

KU KUMA KARANTA: An yankewa mahaifiya hukuncin ɗaurin rai da rai, bisa laifin kashe ‘yarta

Lamarin ya faru ne a daidai ofishin kwastom dake ‘club road’, inda suka yi yunƙurin caka masa wuƙa a ciki, amma Allah ya kiyaye, abin ya same shi a hannu. Wakiliyar Neptune Prime ta zanta da Musa, ga abin da ya ce “zuwa yanzu Alhamdulilh an gyara ciwon an ɗinke min, sai dai raɗaɗin da yatsa na yake yi, ina rokon Allah waɗanda suka min wannan mummunan aikin Allah ya sakamin, Allah ya isar min akan su, domin shi ne maganin duk wani azzalumi. Duk da haka ba su yi nasarar ƙwace wayar ba a hannuna”

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...