No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar ’yan sanda ta kama wasu mutum uku da ake zargin su da fashi da makami da kuma ƙwacen motoci a Abuja.

Kwamishinan ’yan sandan Abuja, Garba Haruna, yayin da yake gabatar da waɗanda ake zargin a hedikwatar ’yan sandan ya ce an kama su ne bayan wani ɗauki-ba-dadi da jami’an rundunar.

Ya ce mutanen ukun na da alaka da yawaitar fashi da makami da ƙwacen mota Abuja.

“An kama su da motoci biyu; Toyota Corolla mai launin toka mara lamba da baƙar Toyota Camry 206, ita ma ba ta da lamba, da kuma bindiga guda ɗaya,” in ji shi.

KU KUMA KARANTA : Yadda za ka kare kanka daga masu ƙwacen Whatsapp

Ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike don gano ragowar da suke aikata laifukan.

Ya kuma tabbatar wa mazauna Abuja cewa, rundunar ’yan sandan na ci gaba da jajircewa wajen samar da tsaro da kwanciyar hankali.

Kazalika, ya buƙaci mazauna Abuja da su kasance cikin shiri da bayar da rahoton gaggawa ga ’yan sanda ta wadannan lambobi domin kai musu ɗauki 08032003913, 08061581938, 07057337658.38.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...