No menu items!

Sample Page Title

Date:

Masarautar Kano ta umarci dukannin hakimai da Ƴan Majalisar Sarki da su shigo birnin Kano domin gudanar da hawan sallah 

Daga Jameel Lawan Yakasai

Masarautar Kano ta Kofar Kudu ƙarƙashin jagorancin Sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sunusi II ta umarci dukkan Hakimai da ke ƙarƙashinta su shigo cikin birnin Kano domin halartar Hawan Babbar Sallah.

Wannan na cikin wata sanarwa da fadar masarautar ta fitar a daren Litinin, inda ta bukaci Hakiman su tabbatar da isowarsu cikin lokaci domin tsara jerin hawan Sallah yadda ya kamata.

KU KUMA KARANTA: ‘Yansanda a Kano, sun gayyaci Shamakin Kano kan zargin saɓa wa umarnin haramta hawan sallah a jihar

Sanarwar ta jaddada cewa wannan umarni ya shafi dukkan masu rike da sarautar gargajiya a cikin Masarautar Kano ta Kofar Kudu.

Bikin Hawan Sallah al’ada ce mai muhimmanci wadda ke tattare da nuna haɗin kai da al’adun gargajiya a tsakanin masarauta da al’ummar gari, inda Sarki da Hakimansa ke gudanar da jerin gwano bayan kammala sallar Idi da wasu ranakun da suke biyo bayan ranar Sallah.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...