No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafsser

Mai Martaba Sarkin Fika, kuma shugaban sarakunan jihar Yobe, Alhaji Muhammad Abali Ibn Muhammad Idris, ya aika Alhaji Ali Adamu Fika ya wakilce shi a wajen ta’aziyyar rasuwar mahaifiyar Dakta Hassan Gimba (mawallafin jaridar Neptune Prime) a gidansu da ke garin Potiskum jihar Yobe, a yau Laraba.

Alhaji Ali ya yi addu’o’i na musamman da fatan Allah jiƙanta da rahama, ya gafarta mata.

Haka kuma Mai Martaba Sarkin Pataskum, Alhaji Umaru Bubaram Ibn Wuriwa Bauya, ya aiko da tawaga ta musamman daga fadarsa domin ta’aziyyar rasuwar Hajiya Hafsat Ahmed.

KU KUMA KARANTA: Gwamnan Yobe ya je ta’aziyyar rasuwar mahaifiyar mawallafin jaridar Neptune Prime

Mai Martaba Sarkin Tikau, Alhaji Muhammad Abubakar Ibn Grema, shi ma ya turo tawaga ta musamman daga fadarsa da ke ƙaramar hukumar Nangere, domin yi wa Dakta Hassan Gimba ta’aziyyar rasuwar mahaifiyarsa.

Jama’a da dama ne suke ta tururuwa zuwa yi masa ta’aziyya. Ciki har da Hakimin Kukuri, Sardaunan Fika, Alhaji Audu Babayo, tsohon ɗan majalisar dattijai da Alhaji Adamu Gwargwar. Sannan akwai tawaga ta musamman daga makarantun CAMTECH da FCE Potiskum.

Sannan a yau ne aka yi addu’ar uku na rasuwar Hajiya Hafsat Ahmed.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...