No menu items!

Sample Page Title

Date:

Masarautar Bauchi ta tuɓe rawanin wasu sarakai shida a yankin Hakimin Galambi.

Jami’in yaɗa labaran masarautar, Babangida Hassan Jahun ya ce majalisar masarautar ta soke naɗin sarakan da abin ya shafa ne saboda Hakimin Galambi bai bi ƙa’ida ba wajen naɗa su.

Ya ƙara da cewa masarautar ta dakatar da Haikimin ne Hakimin Galambi, Alhaji Shehu Adamu Jumba daga yin naɗin sarauta na tsawon shekara guda, daga ranar 7 ga watan Nuwamba, sannan wajibi ne ya bi ka’ida nan gaba wajen yin naɗin sarauta.

KU KUMA KARANTA: Masarautar Adamawa ta tuɓe Hakimin Ribadu

A kwanakin baya ne Hakimin Galambi wanda shi ne Ɗanlawal na Bauchi, ya yi wa wasu mutanen shida naɗin sarautar Galadaman Danlawal, Wakilin Dokan Danlawal da kuma Majidadin Danlawal.

Sauran su ne Wakilin Gonan Danlawal, Sarkin Dajin Danlawal da kuma Hardon Danlawal.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...