No menu items!

Sample Page Title

Date:

Maniyyata 200 kacal suka biya kuɗin hajji a Taraba

Hukumar Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta ware wa jihar kujeru 1,400 domin maniyyatan jihar domin sauke farali a bana, amma mutum 200 kacal suka biya.

Wannan shi ne adadi mafi ƙaranci na maniyyatan aikin Hajji daga jihar.

KU KUMA KARANTA:Hukumar NAHCON ta sanar da kuɗin kujerar Hajjin 2025

Kakakin Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Taraba, Hamza Baba Muri, ya bayyana cewa a bara alhazai 1,007 me suka yi aikin Hajji daga jihar.
Ya ce saboda ƙarancin maniyyatan da suka kammala biyan kudin kujera, hukumar za ta gudanar da gangami a faɗin jihar domin ba wa jama’a ƙwarin gwiwa su biya.

A cewarsa, jami’an hukumar za su karaɗe ɗaukacin ƙananan hukumomin jihar domin wannan aikin neman ƙarin maniyyata.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...