Connect with us

Labarai

Majalisar dokokin Kano ta amince da dokar kare haƙƙin yara

Published

on

A ranar Laraba ne majalisar dokokin jihar Kano ta amince da dokar kare haƙƙin yara ta jihar.

An zartar da ƙudurin dokar ne bayan tattaunawa mai zurfi da kwamitin majalisar ya yi a yayin zaman majalisar wanda mataimakin kakakin majalisar Kabiru Dashi (APC-Ƙiru) ya jagoranta a Kano.

Bayan kammala tattaunawa ne ‘yan majalisar suka amince da karatu na uku na ƙudirin da magatakarda Garba Gezawa ya yi.

KU KUMA KARANTA: Hukumar FRSC ta nemi a kafa dokar shari’ar musulunci ga direbobi masu tuƙin ganganci

Jim kaɗan bayan zartar da ƙudirin dokar, mataimakin shugaban masu rinjaye, Ɗahiru Zarewa (APC-Rogo) ya ce an yi la’akari da shi kuma aka amince da shi bayan an gudanar da ayyukan majalisa daban-daban.

Ya ce an amince da dokar ne saboda jajircewar da ‘yan majalisar suka yi na bunƙasa yara da ci gaban jihar.

“A matsayinmu na wakilan jama’a, mu ne ke da alhakin samar da dokokin gudanar da shugabanci nagari a jihar,” inji shi.

Zarewa ya yabawa ’yan ƙungiyar bisa shigar da masu ruwa da tsaki waɗanda suka ba da gudumuwarsu ga ƙudirin.

A cewarsa, dokar idan aka sanya hannu kan dokar za ta inganta ilimi da duba ayyukan cibiyoyin marayu da kuma batun cin zarafin yara.

Majalisar ta kuma yabawa abokan aikin raya ƙasa bisa goyon bayan da suka bayar wajen ganin an samu nasarar zartar da ƙudirin.

Hakazalika, majalisar ta zartar da ƙudurin dokar asusun kula da tituna na jihar Kano, 2023. Shima da yake jawabi mataimakin shugaban majalisar ya bayyana cewa ƙudirin dokar na da nufin tallafawa hukumar kula da hanyoyin karkara ta jihar.

Ya kuma ce hakan zai taimaka wajen samar da kuɗaɗen gina hanyoyin shiga karkara. “Hukumar, idan aka kafa ta, za ta sauƙaƙe tare da inganta zamantakewar al’umma da tattalin arziƙin jama’a, musamman mazauna yankunan karkara da suke gudanar da ayyukan noma,” inji shi.

Wakilan haɗin gwiwar Ilimin ‘Yan Mata, Kungiyar Mata Musulmi ta Najeriya, FOMWAN, NAPTIP da Hukumar Kare Yara ta Ƙasa, waɗanda suka yi jawabi bayan amincewa da ƙudirin, sun yabawa ‘yan majalisar kan ƙoƙarinsu.

Sai dai sun roƙi gwamnan da ya sanya hannu a kan ƙudirin dokar.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Majalisar Dattawa ta amince da buƙatar Tinubu na naɗa masu ba da shawara na musamman guda 20 | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like