Connect with us

Rasuwa

Mai magana da yawun gwamna Zulum, Isa Gusau, ya rasu

Published

on

Allah Ya yi wa mai magana da yawun Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum rasuwa.

Malam Isa Gusau ya rasu ne a wani asibiti a ƙasar Indiya a jiya Alhamis, inda ya yi doguwar jinya kamar yadda wakilinmu ya ruwaito.

Malam Isa Gusau, ya riƙe muƙamin mai magana da yawun tsohon Gwamnan Jihar Borno, Sanata Kashim Shettima, wanda a yanzu shi ne Mataimakin Shugaban Ƙasar Najeriya.

Bayanai sun ce Malam Isa Gusau ya kwashe sama da wata guda yana jinya a wani asibiti a Indiya.

Majiyar ta ce: “mun rasa Gusau da sanyin safiyar ranar Alhamis inda ya yi kusan kwana uku a sume kafin rasuwar sa.

KU KUMA KARANTA: Ƙungiyar ‘yan jarida ta ƙasa, ta je ta’aziyyar rasuwar mahaifiyar mawallafin jaridar Neptune Prime

“Duk mun yi masa addu’ar samun lafiya, amma Allah bai yarda kuma Ya karɓi abinsa kasancewar Ya fi mu sonsa.”

Makusanta da ke ci gaba da alhini sun bayyana marigayi Isa Gusau a matsayin mutumin kirki da taka-tsan-tsan kan harkokin rayuwa wajen ganin ya sauke nauyin duk wanda ya rataya a wuyansa.

Har yanzu dai ba a bayyana lokacin da za a dawo da gawarsa gida Najeriya ba domin yi masa jana’iza.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Published

on

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu

Daga Ibraheem El-Tafseer

Frane Selak ya kasance wanda ya fi kowa tsallake rijiya da baya a duniya.

A shekarar 1962 ya tsallake haɗarin jirgin ƙasa wanda mutane 17 suka mutu, a 1963 jirgi ya faɗi da shi kowa ya mutu sai shi kaɗai ko ƙwarzane bai yi ba.

A shekarar 1966 motar safa ta lume da su a rafi mutum huɗu sun mutu amma Frane bai samu ko ƙwarzane ba a yayin da a shekarar 1973 motarsa ta kama da wuta ya tsallake rijiya da baya, ya kuma tsallake haɗarin taho mu gama da mota ta yi da shi ya tsira ya kuma lashe yuro dubu ɗari takwas a Caca a shekarar 2003.

KU KUMA KARANTA: Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki

Continue Reading

Rasuwa

Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Published

on

Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Hajiya Zainab ta rasu ne a asibiti  bayan gajeruwar rashin lafiya.

Mutuwa ta riske ta ne a wani asibiti da ke Minna, babban birnin jihar a ranar Talata.

Gwamnan jihar, Mohammed Umaru Bago, ya bayyana alhini da game da wannan rashi.

Sakon ta’aziyyar da kakakinsa, Bologi Ibrahim, ya sa wa hannu ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi ga jihar.

KU KUMA KARANTA: Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Ya kuma yi addu’a Allah Ya sada ta da mafificin rahama a Aljanna Firdausi, Ya ba wa mijinta hakurin jure wannan rashi.

Continue Reading

Rasuwa

Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Published

on

Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa

Mahaifiyar tsohon Gwamnan Jihar Borno, Sanata Ali Modu Sheriff ta riga mu Gidan Gaskiya.

Mahaifiyar tsohon gwamnan, Hajja Aisa, ta koma ta Mahaliccinta ne a ranar Lahadi a Maiduguri, babban birnin jihar.

Ta rasu tana da shekaru 93, bayan fana da rashin lafiya.

Sanarwar rasuwar ta bayyana cewa za yi jana’izar Hajja Aisa da Azahar ranar Litinin 1 ga watan Yuli, 2024.

KU KUMA KARANTA: Allah Ya yi wa tsohuwar jarumar Kannywood, Fati Slow rasuwa

Za a yi jana’izar ne a gidant Marigayi Galadima Modu Sheriff d da ke Damboa Road a Maiduguri.
Sanarwar ta kuma roka wa marigayiyar gafara da kuma Aljannatul Firdaus.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like