No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaban ƙasar Senegal Macky Sall ya taya ɗan takarar jam’iyyar adawa Bassirou Diomaye Faye murnar lashe zaɓen shugaban ƙasar da aka gudanar ranar Lahadi, 24 ga watan Maris.

“Ina yabawa game da yadda aka yi zaɓen shugaban ƙasa na ranar 24 ga watan Maris, 2024 ba tare da matsala ba kuma ina taya murna ga wanda ya yi nasara, Mr. Bassirou Diomaye Faye, wanda alamu suka nuna cewa shi zai yi nasara. Wannan nasara ce da dimokuraɗiyyar Senegal,” in ji Sall a sakon da ya wallafa a shafinsa na X ranar Litinin.

Sall ya fitar da saƙon ne jim kaɗan bayan tsohon Firaministan Senegal kuma ɗan takarar gamayyar jam’iyyu masu mulki ya amsa shan kaye a hannun ɗan takarar jam’iyyar adawa a zaɓen shugaban ƙasa.

KU KUMA KARANTA: Tarihin sabon shugaban ƙasar Senegal, Bassirou Diomaye Faye

Amadou Ba, ɗan takarar jam’iyya mai mulki ya faɗa a wata sanarwa daga ofishin kamfe ɗinsa ranar Litinin, cewa yana taya murna ga ɗan takarar jam’iyyar adawa, Bassirou Diomaye Diakhar Faye, kuma yana yi masa fatan alheri.

Sakamakon farko ya nuna cewa Faye ya samu aƙalla kashi 57 na ƙuri’un da aka kaɗa, yayin da Ba ya samu kashi 31.

Nasarar da ya samu a zagayen farko na zaɓen ta dace da abin da aka gani na yadda mutanen ƙasar ke nuna ɓacin-ransu da rashin aikin-yi da shugabanci nagari a ƙasar da ke Yammacin Afirka.

Diomaye Faye, wanda ke da goyon baya daga shahararren ɗan adawa Ousmane Sonko, ya sha alwashin raba Senegal da rashawa a ɓangaren gwamnati.

Zaɓen da ya gudana ranar Lahadi ya biyo bayan watannin da aka kwashe ana tararrabi da rashin zaman lafiya bayan da shugaba mai ci, Macky Sall ya yi yunƙurin dakatar da zaɓe har zuwa ƙarshen shekara.

Zanga-zangar da ta biyo bayan yunƙurin ta girgiza kyakkyawan sunan da Senegal take da shi a matsayin tsayayyiyar ƙasar dimukurɗiyya a yankin da ya sha fama da jerin juyin mulki a ƴan shekarun nan.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...