Connect with us

Labarai

Ma’aikatan filin jirgin sama na Kano, sun zargi sojoji da yin gini a gaban gidajensu

Published

on

Ma’aikatan filin jiragen sama na Malam Aminu Kano da ke Kano sun gudanar da zanga–zangar lumana don nuna rashin gamsuwarsu da wani gini da Rundunar Sojin Sama take yi a gaban gidajensu.

Sojojin dai na yin gine-ginen ne a gaban gidajen nasu da ke rukunin gidajen na ma’aikatan filayen jiragen sama da ke Kano, wato Aviation Quarters.

Shugaban Harkokin Tsaro da Walwalar Ma’aikatan, Kwamared Muhammad Zakariyya Dauda ya ce sun wayi gari sun ga sojojin sun mamaye unguwar tasu tare da yi musu gini a filin da suke motsa jiki su da ’ya’yansu.

“Muna wajen aiki ne ’yan uwanmu da ke gida suka yi mana waya cewa sojoji sun yi mana kutse a gidajenmu tare da fara gini a filin da ke cikin gidajenumu.

KU KUMA KARANTA: An yi wa ‘yan sanda biyar duka a Abuja, a ƙoƙarin ceton wanda ake zargi da satar mazakuta

“Wannan fili shi ne muke amfani da shi wajen motsa jiki mu da ’ya’yanmu. Ba su tuntuɓe mu ba suka cire mana allon da ke ɗauke da sunan hukumarmu a jiki.”

Haka kuma ma’aikatan sun zargi sojojin da hana su shiga gidajensu tare da dukan wani daga cikinsu a daidai lokacin da yake ƙoƙarin sauƙe ’ya’yansa da ya ɗauko daga makaranta.

“Waɗannan sojojin sun hana ma’aikatanmu shiga gidajensu har ma suka sa kan bindiga suka doki wani ma’akacinmu a lokacin da yake ƙoƙarin shiga unguwar don sauƙe ’ya’yansa da ya ɗauko daga makaranta,” in ji Kwamared Muhammad.

Har ila yau, ma’aikatan sun nemi Shugaban ƙasa da Majalisar ƙasa da duk masu ruwa da tsaki da su sanya baki cikin lamarin don ganin an yi wa tufkar hanci.

Kakakin Rundunar Sojin Sama Air commodore Edward Gabkwet, ya ce zai bincika tare da sanar da manema labarai halin da ake ciki. Amma har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton bai tuntuɓe mu ba.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like