No menu items!

Sample Page Title

Date:

Liverpool ta lallasa Manchester United ci 3 da nema

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Liverpool ta doke abokiyar hamayyarta, Manchester United har gida da ci uku da nema.

Wannan na zuwa ne bayan karawa da ƙungiyoyin biyu suka a gasar Firimiyar Ingila ta bana, a mako na uku.

Manchester United ta yi rashin nasara a wasanni biyu daga cikin uku da ta buga bayan fara gasar Firimiyar ta bana.

KU KUMA KARANTA: Babu rashin jituwa tsakanina da Salah – Klopp

A makon da ya gabata ƙungiyar ta yi rashin nasara da ci 2 da 1 a hannun Brithtom Hove & Albion.

Manchester United ta samu nasara ne a wasa ɗaya kaɗai, inda ta doke Fulham a wasan farko na gasar.

’Yan wasan gaban Liverpool, Luis Diaz da Mohamed Salah ne suka jefa wa ƙungiyar ƙwallon uku.

Yanzu haka Liverpool na mataki na biyu da maki tara a teburin gasar, yayin da Manchester United ke mataki ma 13 da maki 3.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...