No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ministan harkokin cikin gida na Libya, Emad al-Tarabelsi, a ranar Talata ya sanar da cewa an tasa ƙeyar baƙin haure 486 ba bisa ƙa’ida ba zuwa ƙasashensu na asali.

Ministan ya bayyana hakan ne a wani taron manema labarai, inda ya ƙara da cewa 294 daga cikin baƙin haure ba bisa ƙa’ida ba sun fito ne daga ƙasar Masar, yayin da sauran suka fito daga ƙasashen Afirka daban-daban.

Al-Tarabelsi ya ce mutanen da aka kora sun haɗa da waɗanda aka bari a baya-bayan nan a maƙale a kusa da kan iyakar ƙasar Tunusiya bayan da hukumomin Tunisiya suka kore su.

“Dole ne ƙasashen duniya da Tarayyar Turai su taimaka wa Libiya wajen rage wannan al’amari, wanda ya ɗora wa ƙasar nauyi da yawan baƙin haure.

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin Najeriya ta kwashe dukkan ‘yan kasarta da suka maƙale a birnin Khartoum na Sudan

“Ma’aikatar harkokin cikin gida ta ƙaddamar da faɗaɗa yaƙin tsaro na kame masu safarar mutane tare da miƙa su kotu.

Al-Tarabelsi ya ce “Za a ƙara ƙarfi a nan gaba.” Tun bayan hamɓarar da gwamnatin marigayi Mu’ammar Gaddafi a shekara ta 2011, ƙasar da tashe-tashen hankulan da suka addabi ƙasar ta zama wurin da baƙin haure da ke son tsallakawa tekun Mediterrenean zuwa gabar tekun Turai suka fi so.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...