No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan ya musanta rahotannin da kafafen yaɗa labarai suka yaɗa cewa ya shiga takarar neman shugabancin majalisar wakilai ta 10.

Lawan ya bayyana haka ne a wata sanarwa da ya fitar a Abuja ranar Talata.

“Na karanta wasu rahotannin kafafen yaɗa labarai cewa na shiga takarar neman shugabancin majalisar dattawa ta 10.

“A ƙa’ida da ban mayar da martani ga waɗannan rahotanni ba amma idan ba a ƙaryata ba, suna da ɗabi’ar haifar da ruɗani na gaskiya.

KU KUMA KARANTA: Shugabancin majalisar wakilai: Ya kamata mutunta martabar jam’iyya – Anamero Dakeri

“Gaskiyar magana ita ce ban taɓa faɗawa kowa ko ganawa da kowa cewa ni zan tsaya takarar shugabancin majalisar dattawa ta 10 ba, don haka jama’a su yi watsi da waɗannan rahotannin.

“Gaskiyar lamarin dai ina cikin jagorancin babbar jam’iyyar mu ta APC, ina neman ganin an magance ɗimbin matsalolin da suka taso a fafatawar neman shugabancin majalisar wakilai ta 10, kuma zan ci gaba da mai da hankali kan hakan.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...