Connect with us

Ƙasashen Waje

Kwamitin Tsaro na MƊD na buƙatar gyara – Ministan Harkokin Wajen Turkiyya

Published

on

Ministan Harkokin Wajen Turkiyya, Hakan Fidan, ya jaddada buƙatar yin garambawul ga Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya, inda ya bayyana gazawarsa wajen tunkarar al’amuran duniya da suka haɗa da na Gaza.

A rana ta biyu ta taron Ministocin Harkokin Wajen kasashen G20 a Brazil, Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Hakan Fidan ya halarci taron sake fasalin tsarin mulki na duniya a yau Alhamis, inda ya bayyana muhimmancin cibiyoyi masu inganci da kuma ingantattun hanyoyin gudanar da mulki a duniya don magance tashe-tashen hankula na yankuna a cikin sabon tsarin duniya na yau.

Ya ce ya zama wajibi a fahimci buƙatar samun sauyin, kuma ya kamata a ba da fifiko wajen yin garambawul ga Kwamitin Tsaro, a cewar majiyoyin diflomasiyyar Turkiyya.

Fidan ya ce Majalisar ta yi watsi da martabar tsarin MƊD baki ɗaya, kuma ana buƙatar “tsari mai inganci da tsarin dimokuraɗiyya” bisa ƙa’idojin dokokin ƙasa da ƙasa.

Majiyoyin sun ce Fidan ya kuma lura cewa ya kamata tsarin hada-hadar kudi na ƙasa da ƙasa ya kasance “mai haɗo kowa da kowa bisa gaskiya da ƙa’ida kuma mai ɗorewa.”

Ya ce ya kamata cibiyoyin hada-hadar kuɗi na ƙasa da ƙasa da bankunan ci gaban ƙasashe daban-daban su yi amfani da manufofin da suka dace da kasashe masu tasowa da wadanda ba su da ci gaba don cike giɓin da ke tsakanin ƙasashe masu tasowa.

KU KUMA KARANTA: Ministocin Tsaron Turkiyya da Djibouti sun sa hannu kan yarjejeniyar haɗin gwiwa ta soji

Idan ba haka ba, in ji Fidan, ba za a iya cimma burin ci gaba mai ɗorewa ba.

Ya ƙara da cewa G20 na da muhimmiyar rawar da za ta taka wajen taimaka wa lamarin.

Ministan Harkokin Wajen Turkiyya, Hakan Fidan, ya kuma gana da takwaransa na Saudiyya Yarima Faisal bin Farhan Al Saud a yau Alhamis, inda suka tattauna kan halin da ake ciki a Gaza, a cewar majiyoyin diflomasiyyar Turkiyya.

Ministocin sun yi musayar ra’ayi kan matakan da ƙasashen yankin za su iya ɗauka na tsagaita wuta na gaggawa a Gaza, da kuma samar da ƙasashe masu cin gashin kansu na Isra’ila da Falasɗinu, a cewar majiyoyin diflomasiyya.

“Fidan ya sanar da cewa taron Gaza da za a gudanar a taron diflomasiyya na Antalya mai zuwa zai zama “muhimmiyar dama.”

Bugu da ƙari, an tattauna dangantakar da ke tsakanin ƙasashen biyu da tattalin arziki da haɗin gwiwa a fannin tsaron masana’antu, in ji majiyar.

Taron ya zo ne a gefen taron Ministocin Harkokin Wajen Ƙasashen G20 da ake yi a Brazil.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Published

on

Harin ta'addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Wani hari da ake kyautata zaton masu ikirarin jihadi ne suka kai ƙauyen Djiguibombo da ke kusa da garin Bandiagara a yankin tsakiyar ƙasar Mali, ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20, kamar yadda wasu hukumomin yankin biyu suka tabbatar.

Majiyoyin da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da mutuwar mutane 20, sannan suka ce yadda lamuran tsaro suka taɓarɓare a yankin, ya hana jami’an tsaro kai ɗauki wajen.

Wani jagoran matasan yankin shi ma da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce tun a farkon daren ranar Litinin ɗin data gabata ne maharan suka kai farmakin, inda suka kwashe tsawon sa’oi uku a cikin garin.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe ‘yan jarida 106 a yakin da take yi a Gaza — Jami’ai

Ya ce sama da mutane 20 ne aka kashe a harin, kuma fiye da rabinsu matasa ne inda aka ranke musu harsuna.

Kasar Mali dai na fama da matsalolin tsaro na ƙungiyar Al-Qaeda da kuma na IS tun a shekarar 2012, inda ya bazu kasashen Burkina Faso da Nijar da ke makwabtaka da ita.

Tun bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi a kasar a shekarar 2020, hukumomi  ke jin tsoron fitowa fili su sanar da labarin hare-haren ta’addancin da ake kai wa kasar da ke Yammacin Afrika.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Published

on

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama - Ministan Tsaron Isra'ila

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce sojojin Isra’ila za su kasance a shirye don daukar duk wani matakin da ya dace kan ƙungiyar Hizbullah ta ƙasar Labanon, ko da yake abin da ake so shi ne cimma matsaya ta shawarwari.

Muna kai wa ƙungiyar Hizbullah hari sosai a kowace rana kuma za mu kai ga cikakken shiri na ɗaukar duk wani mataki da ake buƙata a ƙasar Labanon, ko kuma cimma wani shiri daga matsayi mai ƙarfi.

KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

Mun fi son tsari, amma idan aka kai mu maƙura za mu san yadda za mu yi yaƙi,” an ruwaito Gallant a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Published

on

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Aƙalla mutum 12 ne suka mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a jiya Laraba a wani hari da aka kai kan wata kasuwar dabbobi da ke El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Yammacin Sudan.

A wata sanarwa da kwamitin sulhu na kwamitocin ‘yan gwagwarmaya na El Fasher ya fitar ya ce “harbin bindigogi a kasuwar dabbobi da ke birnin El Fasher ya yi sanadin mutuwar fararen hula 12 da kuma wasu 20 da suka samu raunuka daban-daban.”

Tun da fari a ranar Larabar da safe, kwamitocin ‘yan gwagwarmaya sun ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai mummunan hari El Fasher da manyan bindigogi.

Tun a ranar 10 ga Mayu, aka fara ƙazamin fada tsakanin sojojin Sudan da RSF a El Fasher. Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa ke amfani da birnin a matsayin cibiyar ayyukan jinƙai ga yankin Darfur.

Rikicin Sudan ya ɓarke ne a cikin watan Afrilun 2023 tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo kan yarjejeniyar shigar da RSF cikin rundunar soja.

KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD

Ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 16,000, da raba kusan mutum miliyan 10 da muhallansu, sannan sama da miliyan 25 na buƙatar agajin jinƙai, lamarin da ya zama mafi girma a duniya ta ɓangaren matsalar rashin matsuguni da yunwa, a cewar MƊD.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like