No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wani rahoto da Ƙungiyar Tarayyar Turai ta fitar, ya tabbatar da cewa kusan mutum 400,000 ne suka mutu a nahiyar Turai, sakamakon shaƙar gurɓatacciyar iska.

Rahoton, ya nuna cewa wannan ibtila’I ya faru ne a shekarar 2021 kaɗai, tare da cewar da an bi dokokin da WHO ta gindaya, da addadin basu kai haka ba.

Hukumar kula da muhalli ta Turai, ta ce a tsakanin ƙasashen Turai kaɗai, gurɓatacciyar iskar da ke shafar mutanen da ke fama da ciwon zuciya, ta yi sanadin mutuwar mutum 253,000 a shekarar 2021 kaɗai.

Gurbatacciyar iskar da ake samu daga sinadarin nitrogen dioxide ko kuma NO2, ta fi shafar mutanen da ke fama da ciwon sukari, inda ta kashe mutum 52,000.

KU KUMA KARANTA: Guguwar iska ta lalata gonakin kaji, ta kashe tsuntsaye dubu uku a Filato

Idan aka haɗa da ƙasashen da ke wajen Turai kuwa, EU ta ce, adadin ya kai 389,000 na waɗanda suka mutu, sakamakon nau’in iskar nitrogen dioxide NO3

A cewar rahoton, dole ne a ɗauki matakan kariya, idan har ana son kawo ƙarshen mace-macen mutanen da ke shakar wannan iska mai haɗarin gaske, musamman a ƙasashe mambobin Ƙungiyar Tarayyar Turai.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...