No menu items!

Sample Page Title

Date:

Sama da mutum 90,000, wato kusan kashi 4 cikin 100 na al’ummar Gaza a halin yanzu ko dai sun mutu ko sun samu rauni ko sun ɓace, kamar yadda wata ƙungiyar kare hakkin bil adama ta bayyana.

Ƙungiyar Euro-Mediterranean Human Rights Monitor ta bayyana haka ne bayan binciken da ta yi dangane da irin hare-haren ta sama da ƙasa da ruwa da ke ci gaba da kaiwa a Gaza waɗanda suka lalata kaso 70 cikin 100 na ababen more rayuwa a birnin.

Ƙungiyar ta zargi Isra’ila da mayar da Zirin Gaza wurin da ba zaman lafiya.

Ɗaruruwan gawarwakin da ba za a iya ɗaukarsu ba sun kasance a kan tituna, a cewar ƙungiyar, musamman a yankunan da sojojin Isra’ila suka kai farmaki ta ƙasa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...