No menu items!

Sample Page Title

Date:

Muƙaddashin Sufeto Janar na ‘yan sandan Najeriya, IGP, Olukayode Egbetokun, ya umurci ma’aikatan lafiya a faɗin ƙasar nan da su yi jinyar waɗanda harbin bindiga ya rutsa da su ba tare da rahoton ‘yan sanda ba.

Egbetokun ya ce umarnin ya zama dole bisa ga Dokar Tilastawa da Kula da waɗanda aka yi wa harbin bindiga, 2017. 

A cikin bayanan cikin gida na ‘yan sanda mai kwanan wata 25 ga Oktoba, 2023, da kuma jawabi ga dukkan Mataimakan Sufeto-Janar na ‘yan sanda, kwamishinonin ‘yan sanda da kwamandojin kwalejojin ‘yan sanda a Ikeja, Kaduna, Oji-River, Maiduguri da Enugu. IGP ɗin ya buƙaci a yaɗa ta sosai domin jama’a su sani suna bin dokar ƙasa.

KU KUMA KARANTA: Shugaban hukumar tsaro ya ajiye aiki kan zargin alaƙa da ‘yan bindiga daga naɗa shi

Yace “Na gabatar da kwafin wasiƙar HMSH&SW/IG/CTCV/ 10/2023 mai kwanan wata 3 ga Oktoba, 2023, da aka samu daga Ma’aikatar Lafiya da Jin Daɗin Jama’a na Tarayya kan batun da ke sama, na rubuta don isar da umarnin Sufeto-Janar.  ‘Yan sandan da kuka bi kuma ku aiwatar da tanade-tanaden Dokar Tilastawa da Kula da waɗanda aka yi wa harbin bindiga na 2017 ba tare da wata shakka ba.

“Sufeto-Janar na ‘yan sandan ya ƙara ba da umarnin cewa ku mai da wannan batu na lakca, kuma ku riƙa yaɗawa domin jama’a su san muna bin dokar ƙasa.”

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...