No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar sojin Najeriya ta yi ƙira ga gwamnonin yankin Arewa da su bai wa sojojin dama domin kawar da ‘yan ta’adda.

Babban hafsan sojin ƙasa, Taoreed Lagbaja ne ya yi wannan roƙo a hedikwatar rundunar da ke Abuja a lokacin da yake karɓar baƙuncin gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal.

Yayin da yake kawar da yiwuwar yin afuwa ga ‘yan fashin da ke addabar yankin Arewa maso yammacin ƙasar nan, Mista Lagbaja ya gargaɗi masu laifin da su fice daga ƙasar nan take.

Bayanin hafsan sojin ya biyo bayan ƙiraye-ƙirayen da tsohon gwamnan jihar, Sani Yerima ya yi a kwanakin baya na cewa a yi wa ‘yan bindigar afuwa.

A cewarsa, Sojoji ba za su bari su shiga wasu sassan ƙasar ba.

KU KUMA KARANTA: Rundunar sojin saman Najeriya ta sake naɗa manyan hafsoshi 98 ​

“Mai girma gwamna, ina ganin muna buƙatar mu duba wannan shirin na afuwa.

Abubuwan da ke aikata laifuka sun tabbatar da cewa ba za a iya gyara su ba.

Don haka, batun yin afuwa ya samar da hanyar da za su sake haɗuwa su sake shiryawa da ƙaddamar da hare-hare,” in ji Mista Lagbaja.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...