Kotun Duniya ta ayyana mamayar da Isra’ila ke yi wa Falasɗinu a matsayin haramtacciya

0
25
Kotun Duniya ta ayyana mamayar da Isra'ila ke yi wa Falasɗinu a matsayin haramtacciya

Kotun Duniya ta ayyana mamayar da Isra’ila ke yi wa Falasɗinu a matsayin haramtacciya

Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa (ICJ) a ranar Juma’a ta yanke hukuncin cewa yankunan Falasɗinawa da aka mamaye sun zama “yanki ɗaya,” wanda za a ba shi kariya da mutuntawa.

Da take jaddada cewa dokokin Hague sun zama wani bangare na dokokin kasa da kasa na al’ada, don haka suna aiki akan Isra’ila, kotun ta ce, “Kariyar da Yarjejeniyar Kare Hakkokin Ɗan’adam ke bayarwa ba ta gushewa idan ana rikici ko kuma mamaya.”

Dangane da mamayar da Isra’ila ta yi wa yankunan Falasɗinawa, kotun ta yi nuni da cewa, “cin gajiyar albarkatun kasa” da Isra’ila ke yi a yankin Falasɗinu da ta mamaye, “ya saɓa da wajibcinta” na mutunta ‘yancin Falasɗinawa.

Musamman kan korar da aka yi a Gabashin Ƙudus da Yammacin Gaɓar Kogin Jordan, kotun ta jaddada cewa manufofin Isra’ila da ayyukanta sun saɓa wa yarjejeniyar Geneva ta 4 na haramcin miƙa mutanen da aka tsare ta tilas.

KU KUMA KARANTA: Kotun duniya ta umurci Isra’ila ta dakatar da kai farmaki a Rafah

“Manufar sasantawa da Isra’ila ta saɓa wa yarjejeniyar Geneva ta 4,” in ji ta.

Kotun ta ce manufofin Isra’ila da ayyukanta sun sa ta mamaye yankunan Falasdinawa, kuma ba ta da ƙwarin gwiwa cewa tsawaita dokar Isra’ila zuwa Gabar Yammacin Kogin Jordan da kuma Gabashin Birnin Ƙudus ya dace.

Kotun ta ICJ ta kuma ci gaba da cewa, Isra’ila ta sami damar yin amfani da muhimmin iko a kan Gaza duk da janyewar sojojinta a shekarar 2005.

Mamayar da Isra’ila ta kwashe shekaru da dama tana yi wa yankunan Falasɗinawa haramun ce kuma ana bukatar kawo karshenta “cikin sauri kamar yadda zai yiwu”, a cewar babbar kotun ta MƊD a yau Juma’a.

“Kotun ta gano cewa ci gaba da zaman Isra’ila a yankin Falasɗinu haramun ne,” in ji alkalin kotun ICJ Nawaf Salam a ranar Juma’a, inda ya ƙara da cewa: “Dole ne Isra’ila ta kawo ƙarshen mamayar cikin hanzari.”

“Kotun ta gano cewa ci gaba da kasancewar Isra’ila a yankin Falasɗinawa da ta mamaye haramun ne,” in ji Salam.

ICJ ta umurci Isra’ila da ta biya “cikakkiyar diyya”, ga dukkan Falasɗinawa kan duk wani “ba daidai ba” da ta yi musu a karkashin mamayar tun shekarar 1967.

Karamin Ministan Harkokin Wajen Falasɗinu Varsen Aghabekian Shahin ya ce wannan “babbar rana ce ga Falasɗinu” bayan da babbar kotun Majalisar Ɗinkin Duniya ta yanke hukuncin mamayar da Isra’ila ta yi na tsawon shekaru da dama da suka wuce ba bisa ka’ida ba.

“Wannan babbar rana ce ga Falasɗinu, a tarihi da kuma bisa doka,” kamar yadda ya shaida wa AFP, yayin da yake magana a madadin Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasɗinu.

“Wannan ita ce hukumar shari’a mafi girma a duniya kuma ta gabatar da cikakken nazari kan abubuwan da ke faruwa ta tsawon lokaci na mamayar da Isra’ila ke yi wa yankin Falasdinu wanda ya saɓa wa dokokin kasa da kasa.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here