No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wani mutum ya tsinci kansa a gidan yari bayan an kai shi kotu bisa zargin yi wa wata ’yar shekara 50 fyade.

Babbar kotun jihar Edo ce ta tasa ƙeyarsa zuwa gidan yari zaman sauraron hukunci.

Kamfanin Dillacin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa wanda ake tuhuma ya musanta zargin da ake masa na yunkurin yi wa dattijuwar mai shekara 50 da haihuwa fyaɗe.

Lauya mai shigar da ƙara, Misis Ama Iyamu, ta shaida wa kotun cewa a ranar 27 ga Maris, 2023, a birnin Benin ne wanda ake zargin ya yi yunkurin yi wa matar fyaɗe.

KU KUMA KARANTA: Wani ya yi wa ƴar shekara 9 fyaɗe kuma ya kashe ta 

Barista Iyamu ta ce, wannan laifi ya saba wa sashe na 4 na dokar cin zarafin jama’a ta jihar Edo, ta 2021, kuma laifin na da hukunci  a sashe na 5 (2) na wannan doka.

Bayan sauraron ƙarar ne Mai Shari’a Efe Ikponmwonba, ta bayar da umarnin a tsare wanda ake zargi a gidan yari

Ta kuma dage sauraron ƙarar zuwa ranar 8 ga watan Yuli  2024.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...