No menu items!

Sample Page Title

Date:

Kotu ta yanke wa ’yan canji 17 a Kasuwar WAPA da ke Kano hukuncin daurin wata shida a gidan yarin.

Mai Shari’a Muhammad Nasir Yunusa na Babbar Kotun Jihar Kano ya yanke musu hukunci ne bayan samun su da laifin aiki babu lasisi.

Sai dai kotun ta ba su zaɓin biyan tarar naira dubu 50 bayan sun amsa laifin da aka gurfanar da su a kai.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda sun tsare ’yan canji 17 a kasuwar WAPA

A makon jiya cewa ’yan sanda da jami’an hukumar tsaro ta DSS sun kai samame a Kasuwar WAPA, inda suka kama wasu ’yan canji 17 kan zargin laifin aiki babu rajista.

A lokacin samamen jami’an tsaron sun kama kuɗaɗen ƙasashen waje da suka hada da Sefa 68,000 da kuma Rupee 30,000 a hannunsu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...