Connect with us

Ƙasashen Waje

Kenya ta soma sauraron ƙararraki kan zargin cin zarafi da sojojin Birtaniya suka yi

Published

on

Kenya ta soma sauraron ƙararraki kan zargin cin zarafi da sojojin Birtaniya suka yi

Kenya ta soma sauraron ƙararraki kan zargin cin zarafi da sojojin Birtaniya suka yi

Kenya za ta soma zaman sauraren ƙararrakin jama’a a ranar Talata kan zargin take hakkin ɗan’adam da kuma cin zarafi da sojojin Birtaniya suka yi a kasar wadda ta taba yi wa mulkin mallaka.

Sashen horar da sojojin Birtaniya a Kenya (BATUK) wuri ne na tafiyar da ayyukan da suka shafi tattalin arzikin mutane da dama a tsakiyar garin Nanyuki, inda aka kafa sansanin soji na dindindin, amma kuma ana zargin sojojin da ke wurin da aikata laifuka ciki har da kisan kai.

Ɗaya daga cikin manyan laifuka da suka fi ɗaukar hankali a shekarar 2012, shi ne na tsintar gawar wata mata ‘yar ƙasar Kenya a cikin wata rijiya a Nanyuki, inda ganinta da rai na ƙarshe da aka yi tare da wani Sojan Birtaniya ne.

Iyalan Agnes Wanjiru sun shigar da ƙara a Kenya kan mutuwar matashiyar mai shekaru 21, amma babu wani ci gaba da suka samu kan shari’ar, inda aka yi ta ɗage sauraron ƙarar.

Yanzu dai ana sa ran sake sauraron ƙarar a ranar 10 ga watan Yuli kamar yadda kafafen yada labarai na ƙasar suka rawaito.

A makon jiya ne majalisar dokokin Kenya ta sanar da cewa za ta gudanar da zaman sauraron ƙararrakin jama’a har guda hudu ciki har da na Nanyuki kan cin zarafin da ake zargin sojojin Birtaniya da aikatawa a ƙasar.

Za a yi zaman sauraron ƙararrakin ne tsakanin ranakun Talata da Alhamis na wannan makon inda za gudanar da ”bincike kan zarge-zargen take hakkin bil’adama da suka haɗa cin zarafi da azabtarwa da tsare mutane ba bisa ka’ida ba da kuma kashe- kashe,” a cewar wata sanarwar da majalisar ta fitar.

KU KUMA KARANTA: Ana fargabar zaftarewar ƙasa ta rutsa da mutane da dama a Kenya

Kazalika zaman zai yi duba kan “zargin take hakkokin ɗa’ar aiki da suka haɗa da cin hanci da rashawa da aikata zamba da kuma nuna wariya da cin zarafi da sauran munanan dabi’u.”

Birnin Landan da Nairobi suna takun-saƙa kan batun hukunta sojojin Birtaniya da suka take dokokin Kenya, inda a baya gwamnatin Birtaniya ta ce ba ta amince da hurumin kotun Kenya na bincike kan kisan Wanjiru ba.

Da yake amsa tambayoyi kan sauraron karar na wannan makon, mai magana da yawun hukumar Biritaniya ya shaida wa kamfanin dillacin labarai AFP cewa: “Hukumar Birtaniya a Nairobi da BATUK suna da niyyar ba da hadin kai ga binciken.

“Haɗin gwiwar ayyukan tsaro na Birtaniya da Kenya na ɗaya daga cikin manyan ginshiƙan dangantakarmu kuma horon da muke samarwa ta haɗin gwiwa da ayyukan da muke yi tare suna taimakawa wajen samar da tsaro ga al’ummar Kenya da Birtaniya,” in ji shi.

A ranar Alhamis din da ta gabata ne tawagar Birtaniya ta ce babban kwamishinanta Neil Wigan ya gana da iyalan Wanjiru, waɗanda suka dade suna neman a yi musu adalci kan kashe ta da aka yi.

“Taron ya ba da dama ga Babban Kwamishinan ya saurari ‘yan’uwan marigayiyar tare da yi musu ta’aziyya. Kazalika ya samu damar jaddada matsayar Birtaniya na ci gaba da bayar da cikakken haɗin kanta ga binciken da Kenya ke yi kan (mutuwar Misis Wanjiru),” in ji sanarwar.

A watan Oktoban 2021 ne, Jaridar ‘The Sunday Times’ ta Biritaniya ta ruwaito cewa wani soja ya shaida wa abokansa cewa sun kashe Wanjiru kuma ya nuna musu gawarta.

Rahoton ya yi zargin kan cewa an sanar da manyan jami’an soji game da kisan, amma ba a dauki wani mataki akai ba.

An ƙaddamar da bincike kan batun ne a shekarar 2019 amma ba a bayyana sakamakon ba ga al’ummar.

‘Yan sandan Kenya sun sanar da cewa za a sake buɗe binciken bayan rahoton da Jaridar Sunday Times ta fitar.

Iyalan Wanjiru sun shigar da karar sojojin Birtaniya a Kenya da kuma ‘yan sanda da jami’an shari’a da na siyasa na Kenya kan batun mutuwarta.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Turkiyya ta yi tur da kalaman ministan Isra’ila kan Shugaba Erdogan

Published

on

Turkiyya ta yi tur da kalaman ministan Isra'ila kan Shugaba Erdogan

Turkiyya ta yi tur da kalaman ministan Isra’ila kan Shugaba Erdogan

Ma’aikatar Harkokin Wajen Turkiyya ta yi Allah wadai da wani saƙo da Ministan Harkokin Wajen Isra’ila, Israel Katz ya wallafa a shafukan sada zumunta a baya-bayan nan kan shugaban ƙasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan, inda ta bayyana hakan a matsayin wani yunƙuri na Isra’ila na ɓoye laifukanta.

Sanarwar da Ma’aikatar Harkokin Wajen Turkiyya ta fitar a ranar Talata ta ce “Muna daukar wannan matsayi na rashin mutuntawa da Ministan Harkokin Wajen Isra’ila ke yi wa mai girma shugaban kasarmu a matsayin wani lamari da za a ji shi ne kawai daga bakin ƙasar da ake zarginta da kisan kiyashi.”

Yayin da take suka da kakkausar murya a shafukan sada zumunta, ma’aikatar ta ce: “Irin wannan ƙazafi da ƙarya wani ɓangare ne na ƙoƙarin Isra’ila na ɓoye laifukan da ta aikata.”

Turkiyya ta ƙara da cewa, za ta ci gaba da fafutukar tabbatar da zaman lafiya da adalci.

KU KUMA KARANTA: Ana lalata mutuncin bil’adama a Gaza – Ministan Turkiyya

Isra’ila, wadda ta yi fatali da ƙudurin Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da ke neman tsagaita wuta cikin gaggawa, ta fuskanci tofin Allah-tsine a tsakanin kasashen duniya a ci gaba da kai munanan hare-hare kan Gaza tun ranar 7 ga Oktoba, 2023.

Fiye da Falasɗinawa 37,700 aka kashe tun daga lokacin a Gaza, yawancinsu mata da yara, kuma kusan wasu 86,400 sun jikkata, a cewar hukumomin lafiya na yankin.

Sama da watanni takwas da yakin Isra’ila a Gaza, inda yankuna da dama suka zama kufai a cikin yankin da aka yi wa ƙawanya da hana shigar da abinci da ruwan sha da magunguna.

Ana tuhumar Isra’ila da aikata kisan kiyashi a Kotun Duniya, wanda hukuncin na baya-bayan nan ya umarci Tel Aviv da ta dakatar da kai hare-hare a kudancin birnin Rafah, inda Falasɗinawa sama da miliyan guda suka nemi mafaka daga yakin kafin a mamaye shi a ranar 6 ga watan Mayu.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Shugaba Ruto na Kenya ‘ba zai’ sa hannu a kan sabuwar dokar ƙarin haraji ba

Published

on

Shugaba Ruto na Kenya 'ba zai' sa hannu a kan sabuwar dokar ƙarin haraji ba

Shugaba Ruto na Kenya ‘ba zai’ sa hannu a kan sabuwar dokar ƙarin haraji ba

Shugaban Kenya, William Ruto ya ce ba zai rattaba hannu kan wata doka mai cike da cece-kuce da ta haifar da zanga-zanga a faɗin ƙasar ba, har aka harbe mutane da dama.

Masu zanga-zangar sun mamaye majalisar ne bayan da ‘yan majalisar suka zartar da dokar a ranar Talata. Kudirin zai kara yawan haraji da kuma tsadar rayuwa.

“Bayan yin la’akari da ci gaba da tattaunawa game da abubuwan da ke ƙunshe a cikin kudirin kudi na 2024, da kuma sauraron jama’ar Kenya, wadanda suka yi kira da babbar murya cewa ba sa son wani abu da wannan ƙudirin kuɗi na 2024, na yarda, don haka ba zan sanya hannu ka dokar ba, kuma daga baya za a janye shi,” Ruto ya shaida wa taron manema labarai a fadar gwamnati da ke Nairobi babban birnin ƙasar.

KU KUMA KARANTA: Adadin waɗanda suka mutu a tarzomar Kenya ya ƙaru

“Mutane sun rasa rayukansu kuma abin takaici ne matuka, da ma hakan bai faru ba,” ya ƙara da cewa.

Zanga-zangar ta jawo gwamnati ta girke sojoji don shawo kan karya doka da oda.
Sai dai wata Babbar Kotu ta soke umarnin girke sojojin.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Adadin waɗanda suka mutu a tarzomar Kenya ya ƙaru

Published

on

Adadin waɗanda suka mutu a tarzomar Kenya ya ƙaru

Adadin waɗanda suka mutu a tarzomar Kenya ya ƙaru

Ƙungiyar likitoci ta Kenya ta ce adadin waɗanda suka mutu, sanadiyar zanga-zangar ƙarin kuɗin haraji da gwamnatin ƙasar ta sanar, ya ƙaru zuwa 13.

Shugaban Ƙungiyar Simon Kigondu ne ya tabbatarwa Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP adadin, a wata zantawa da suka yi da shi a yau Laraba.

Masu zanga-zangar waɗanda yawancinsu matasa ne, sun mamaye zauren majalisar dokokin kasar a jiya Talata, inda suka rinka jifar ‘yan sanda da duwatsu da kuma rushe shingen jami’an tsaro don kutsa kai cikin harabar majalisar.

Bayan faruwar lamarin, shugaban ƙasar William Ruto ya tura da jami’an soji don tarwatsa masu zanga-zangar.

KU KUMA KARANTA: Mutum 12 sun mutu a rikicin da ya biyo bayan zaɓen shugaban ƙasa a Chadi

Shugaba Ruto ya lashi takobin ɗaukar tsauraran matakai don tabbatar da zaman lafiya a ƙasar, inda ya sha alwashin hukunta wadanda ke da hannu a lamarin.

Sai dai duk da ɗaukar wancan mataki, masu zanga-zangar sun ce babu gudu babu ja da baya game da ƙudirinsu na ci gaba da zanga-zangar, har sai haƙarsu ta cimma ruwa.

Wani jami’i a asibitin Kenyatta da ke birnin Nairobi, ya ce a asibitin kadai, jami’insu sun duba mutane 160 da suka samu raunukan harhasai wasu kuma kananan raunuka.

Ɗaya daga cikin abubuwan da masu zanga-zangar ke buƙata shi ne shugaban ƙasar William Ruto ya sauka daga muƙaminsa.

Matasan sun bayyana matakin gwamnatin Ruto na lafta wa jama’a haraji a matsayin wani sabon yunƙuri na jefa al’umma cikin ƙarin musiba, ganin yadda tuni matsalar tsadar rayuwa ta yi musu dabaibayi.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like