Connect with us

Al'ajabi

Karnuka sun kashe jariri, sun raunata uwa a Osun

Published

on

An zargi wasu karnukan Alsatiya guda biyu sun kaiwa wata uwa mai shayarwa mai suna Mummy Basira hari tare da kashe ‘yarta a Unguwar Halleluyah dake Ido-Osun a jihar Osun.

Jaridar Punch ta ruwaito lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe uku na ranar Laraba, 30 ga Agusta, 2023.

Wata majiya da ba a bayyana sunanta ba ta ce Mummy Basira na tafiya kan titi da jaririnta a maƙale a bayanta lokacin da ake zargin karnukan sun fito daga ginin mai gidansu ne suka far mata.

Karnukan sun far wa uwar mai shayarwa ne a lokacin da take ƙoƙarin ceto jaririnta mai watanni biyar.

KU KUMA KARANTA: Hatsarin mota ya kashe mutum ɗaya a Bauchi

Mazauna yankin da suka zuba ido ba tare da wani taimako ba a lokacin da karnukan suka kai hari sun bayyana cewa bayan kashe jaririyar, karnukan sun far wa mahaifiyar, inda suka yi mata mummunar illa.

“Dukkanmu mun yi kallo ba tare da komai ba.
An shaida mana cewa karnukan sun yi tsalle daga wani gini da ba kowa a halin yanzu, suka kama jaririyar, inda aka ce ya kai kimanin watanni biyar ɗaure a baya, suka yi mata kaca-kaca.

“Yayin da karnukan suka kama jaririyar, mahaifiyar ta yi ƙoƙarin ceto ta amma ta ka sa. Bayan kashe jaririn, karnukan sun far wa mahaifiyar, inda suka yi mata raunika da dama.

Daga baya wasu mazauna garin sun yi amfani da sanduna wajen fatattakar karnukan tare da ceto mahaifiyar.

An garzaya da ita wani asibiti a nan Osogbo.

“Gidan da karnukan suka fito ba kowa ba ne, amma mazauna wurin sun san waɗanda suke ziyartar wurin.

Suna ta ƙiran lambobin wayarsu, amma an kashe layinsu. A halin yanzu dai tashin hankali ya yi yawa a unguwar. Mun kai rahoton lamarin a ofishin ‘yan sandan Estate da ke Osogbo,” in ji ganau Da yake tabbatar da faruwar lamarin, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Osun, Yemisi Opalola, ya bayyana cewa ana ƙoƙarin cafke masu karnukan.

Ta ce rundunar ‘yan sanda za ta ga an yi adalci a cikin wannan hali.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Al'ajabi

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Published

on

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano a arewacin Najeriya ta ce ta kama wani mutum da ake zargi da cinna wa wani masallaci wuta yayin da mutane ke Sallar Asuba ranar Laraba.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Gadan da ke Ƙaramar Hukumar Gezawa a jihar ta Kano, da misalin karfe 5:20 lokacin da ake sallah, a cewar sanarwa ‘yan sanda.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar wa da TRT Afrika Hausa faruwar lamarin da kama mutumin da ake zargi, sai dai ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike.

Abdullahi Kiyawa ya ce bincike ya nuna cewa mutumin da ake zargi da cinna wutar Shafi’u Abubakar mai kimanin shekaru 38 ya jefa wata roba ne ɗauke da fetur cikin masallacin, sannan ya cinna wuta.

KU KUMA KARANTA: Mahara a Anambara sun ƙona fadar babban Basarake ƙurmus

Kakakin ‘yan sandan ya ce mutum 24 ne suka ƙone a masallacin, da suka haɗar da manya 20, yara huɗu.

An garzaya da duka waɗanda suka jikkata zuwa asibiti don ba su kulawa, amma babu wanda ya mutu a haɗarin, a cewar sanarwar ‘yan sandan.

Continue Reading

Al'ajabi

An tsinci gawar wata ɗaliba a cikin ɗaki a Kano

Published

on

An tsinci gawar wata ɗaliba mai suna Aisha Yahaya ta Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Ɗangote da ke Wudil, a wani gida da ke wajen jami’ar.

Aisha, ɗaliba ce da ke matakin karatu na uku wato ‘level 300’ a sashen nazarin Kimiyya da Fasahar Abinci na jami’ar wadda aka tsinci gawarta bayan ta koma ɗakinta.

An ce ɗalibar ta rubuta jarrabawarta ta farko a zangon karatun na farko da ake yi a jami’ar.

Wasu daga cikin abokan karatunta sun danganta mutuwarta da shiga cikin matsi da damuwa a dalilin karatu da kuma zana jarrabawar.

A cikin wasiƙar ta’aziyyar, hukumar jami’ar ta bayyana matuƙar baƙin cikinta dangane da rasuwar Aisha Yahaya.

KU KUMA KARANTA: An tsinci gawar wani mutum a kan titi a Kano

Sanarwar ta ce, “Aisha ɗaliba ce mai hazaƙa wadda ta rasu a dalilin bugun zuciya. Za a riƙa tunawa da ita a kan sha’awarta na karatu da jajircewarta kan harkokin karatunta.”

Jami’ar ta ƙara da cewa, ba a iya gano wata da ke tattare da ita ba gabanin mutuwarta saboda ba ta nuna alamun rashin lafiya ko fama da wata cuta ba.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like