No menu items!

Sample Page Title

Date:

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Jos (JED) ya shawarci abokan hulɗarsa a Jihar Gombe da kada su biya kowa kuɗin gyara na’urar taransfoma a yankunansu.

Babban jami’in tsaro na JED, Musa Abdullahi, ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) a ranar Litinin cewa, ba hakkin kwastomomi ba ne su gyara taransfoma idan ta lalace.

Abdullahi ya ce ana sa ran jama’a su kai rahoto ofishin JED mafi kusa a duk lokacin da na’urar taransifoma ta samu matsala, kuma kada su biya wani jami’inta kuɗin gyara.

Ya ce ba daidai ba ne a nemi al’umma su ba da gudummawar kudi don gyara ko canza taransfomarsu da ta lalace, hasali ma yaudara ce da kamfanin ba zai lamunta ba.

Jami’in ya shawarci al’ummar jiha da su kai rahoton duk wani ma’aikacinsu da ya nuna irin wannan buƙata domin ɗaukar matakin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: Najeriya ta maida wa Nijar wutar lantarki

Ya ce “Ba ma karɓar kuɗi daga hannun al’umma don gyara tiransifoma don haka babu wanda ake tsammanin zai biya.

“Duk ma’aikacin da ya je wurin al’umma karbar kudi a gida-gida ko a kan titi, yaudara ce kuma mun haramta hakan.

“Idan kuna ganin ba za ku iya jira a gyara taransfoma ba, sai ku rubuta wa Manajan Darakta ta hannun Manajan Yankinku cewa kuna son tallafa wa kamfanin don radin kanku ba tilasta muku aka yi ba.

Abdullahi ya kuma yi ƙira ga al’ummar Gombe da su mara wa kokarin kamfanin na kare wutar lantarki a jihar.

Sannan ya yi ƙira da kada a rika cin zarafin jami’an JED da ke bakin aiki, yin hakan laifi ne.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...