No menu items!

Sample Page Title

Date:

Kamfanin NNPCL ba zai taɓa ha’intar Najeriya ba – Mele Kyari

Shugaban Kamfanin Man Fetur na Najeriya NNPCL, Mele Kyari ya ce babu ruwan jami’an kamfanin a shigar da man fetur da dangoginsa marar kyau cikin ƙasar.

Kyari ya faɗi hakan ne a yayin da yake bayani a ranar Laraba a Abuja a gaban wani kwamitin Majalisar Dattijai ƙarƙashin jagorancin Sanata Opeyemi Bamidele kan zargin da ake yi cewa ana yi wa fannin man fetur ɗin ƙasar zagon ƙasa.

Kyari ya ce a matsayinsa na shugaban kamfanin NNPCL, ya fuskanci hare-haren da ba su dace ba daga kafafen yada labarai daga mutanen da ke yin duk abin da zai haifar da tunanin cewa NNPCL na yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa.

KU KUMA KARANTA: Ƙaramin Ministan Man Fetur na neman sasanta NNPC da Ɗangote

Ya ce, kamfanin ba zai taɓa ha’intar Najeriya ba kuma ba zai yi ƙarya ba.

“Mu ba masu aikata miyagun laifuka ba ne kuma mu ba ɓarayi ba ne. Dole mu kare martabarmu don mu yi wa ƙasar nan hidima,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa masana’antar man fetur da iskar gas tana tafka asara kuma akwai abubuwan da ya sani amma ba zai iya magana a kansu ba a bainar jama’a har sai “lokacin yin hakan ya yi”.

Kyari ya nemi a watsa zaman kwamitin a talabijin kai tsaye a nan gaba don ‘yan Najeriya su shaida me yake faruwa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...