No menu items!

Sample Page Title

Date:

June 12: Tinubu zai yi wa ƴan ƙasa jawabi gobe

Daga Jameel Lawan Yakasai

Shugaban kasa Bola Tinubu zai yi jawabi ga kasa da misalin karfe 7 na safe ranar Alhamis a matsayin wani bangare na bukukuwan ranar Dimokuraɗiyya ta shekarar 2025.

Tinubu zai kuma halarci zaman hadin gwiwa na Majalisar Tarayya.

Kwamitin bikin ranar dimokuraɗiyya ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Laraba.

KU KUMA KARANTA: Jawabin mataimakin shugaban ƙasa a taron ranar ‘yansanda ta ƙasa a Abuja

Abdulhakeem Adeoye, wanda ya fitar da sanarwar a madadin Daraktan Yada Labarai da Hulda da Jama’a na kwamitin, ya ce bayan jawabin da shugaban kasa zai yi, zai halarci zaman hadin gwiwa na Majalisar Tarayya da misalin karfe 12 na rana.

Sai dai, a cewar Adeoye, ba za a gudanar da bikin faretin Ranar Dimokuraɗiyya ba. Daga bisani a ranar, za a gudanar da muhawara ta musamman dangane da bikin ranar Dimokuraɗiyya a Dakin Taro na Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja da misalin karfe 4 na yamma.

Taken wannan muhawara shi ne: “Ƙarfafa Nasarorin Dimokuraɗiyyar Najeriya: Bukatar Sauye-sauye masu Dorewa.”

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...