No menu items!

Sample Page Title

Date:

Jirgin sojin Najeriya ya faɗo a Kaduna

Wani jirgin sama na sojin Najeriya ya yi hatsari a ƙauyen Tami da ke yankin Karamar Hukumar Igabi a Jihar Kaduna.

Wani mazaunin yankin ya ce jirgin sojin mai sauƙar ungulu ne, kuma ya yi hatsari ne da misalin karfe 5 na asubar Litinin din nan.

Mazauna yankin sun bayyana cewa matukin ya fito daga cikin tarkacen jirgin da ya fado.

Bayan nan sojoji suka yi gaggawar zuwa suka yi wa yankin kawanya tare da fara bincike.

Sojojin sun kuma hana mutane isa wurin da tarkacen jirgin yake.

KU KUMA KARANTA: Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin jirgin samanta

An ce jirgin yana tsaka da aikin sintiri a yankin ne ya samu matsala, lamarin da ya haddasa faduwarsa.

Kawo yanzu Hedikwatar Rundunar Sojin Sama ta Najeriya ba ta fitar da sanarwar game da lamarin ba.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...