Connect with us

Hatsari

Jirgin sojin Najeriya ya faɗo a Kaduna

Published

on

Jirgin sojin Najeriya ya faɗo a Kaduna

Jirgin sojin Najeriya ya faɗo a Kaduna

Wani jirgin sama na sojin Najeriya ya yi hatsari a ƙauyen Tami da ke yankin Karamar Hukumar Igabi a Jihar Kaduna.

Wani mazaunin yankin ya ce jirgin sojin mai sauƙar ungulu ne, kuma ya yi hatsari ne da misalin karfe 5 na asubar Litinin din nan.

Mazauna yankin sun bayyana cewa matukin ya fito daga cikin tarkacen jirgin da ya fado.

Bayan nan sojoji suka yi gaggawar zuwa suka yi wa yankin kawanya tare da fara bincike.

Sojojin sun kuma hana mutane isa wurin da tarkacen jirgin yake.

KU KUMA KARANTA: Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin jirgin samanta

An ce jirgin yana tsaka da aikin sintiri a yankin ne ya samu matsala, lamarin da ya haddasa faduwarsa.

Kawo yanzu Hedikwatar Rundunar Sojin Sama ta Najeriya ba ta fitar da sanarwar game da lamarin ba.

Hatsari

Wani mummunan hatsari yayi sanadiyyar mutuwar mutane 16 daga cikin 18 da ke motar

Published

on

Wata motar fasinja da ta taso daga Bauchi ta yi hatsari a Inugu kuma mutum 16 daga cikin fasinjoji 18 dake motar maza 14 mata 2 sun mųțtu, wasun su ma ba a iya gane su don sun ƙone ƙurmus.

‘Yan sanda sun ce lamarin ya faru da yammacin jiya Talata, 30 ga watan Afrilu a babban titin garin Ekwegbe.

KU KUMA KARANTA: Fasinjoji sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a Kogi

Motar ƙirar Toyota Hummer Bus ce 18 seater dauke da lambar Bauchi, DAS 215 XA, kuma an rubuta “Masha Allah” a jikin motar.

Don haka Kwamishinan yan sanda na Enugu ke roƙon jama’a duk wanda Allah yasa ya san wani daga cikin fasinjojin to a tuntubi rundunar a 08098880172 ko 08086671202

Continue Reading

Gobara

Mutane da dama sun mutu, sakamakon fashewar tankar mai a Fatakwal

Published

on

Ana fargabar mutane da dama sun rasa rayukansu bayan da wata tankar mai ta kama da wuta a hanyar East-West Road a birnin Fatakwal da ke jihar Rivers a kudancin Najeriya.

Jaridun Punch da na Vanguard sun ruwaito cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 9:45 na daren Juma’a.

Bayanai sun yi nuni da cewa bayan da tankar ta mai ta kama da wuta, ta shafi motoci aƙalla goma da ke jerin cunkoson ababen hawa a birnin na Fatakwal.

KU KUMA KARANTA:Matatar man Fatakwal za ta koma bakin aiki cikin watan Afrilu – Kyari

Wani da ya shaida lamarin ya faɗawa jaridar Vanguard cewa ya ji ƙara har sau biyu masu firgitarwa daga baya kuma hayaƙi ya turnuƙe sararin samaniya.

“Idan kuna da ‘yan’uwa a Fatakwal ku ƙira su don ku ji lafiyarsu” Wani mazaunin birnin na Fatakwal mai suna Bassey Esang Don, ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto ba a san musabbabin fashewar da ta auku ba ko iya sanin adadin mutanen da suka mutu.

Faɗuwar tankar mai ta kama da wuta ba baƙon abu ba ne a Najeriya, inda a wasu lokuta mutane kan yi rububin zuwa kwasar man idan yana Malala.

Daga nan ne kuma akan samu akasi har wuta ta kama ta laƙume rayukan mutane.

Wannan al’amari na faruwa ne yayin da farashin mai ya ƙara tsada a Najeriya inda litar mai ta kusa kai wa Naira 1,000 a sassan ƙasar.

Continue Reading

Hatsari

Fasinjoji sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a Kogi

Published

on

Wasu fasinjoji sun ƙone ƙurmus a safiyar wannan Lahadin a dalilin wani mummunan haɗari da ya afku a  garin Aloma da ke Ƙaramar Hukumar Ofu a Jihar Kogi.

Wani shaidan gani da ido ya bayyana cewa haɗarin wanda ya afku a gaban Kwalejin Koyarwa ta Aloma, inda ya rutsa da motocin bas guda biyu da wata motar tirela.

Majiyar ta ce, wata motar bas ƙirar Siena ce cike da fasinjoji ta yi karo da wata motar Toyota da ketahowa a ƙoƙarin kaucewa ramuka da ke kan titin kuma nan take ta kama wuta, lamarin da ya sa dukkan fasinjojin da ke cikin motar suka ƙone.

“Dukkan fasinjojin da ke cikin motar Toyota, ciki har da direban sun ƙone ƙurmus.

KU KUMA KARANTA: Mutane 7 sun ɓace bayan hatsarin jiragen helikwaftan sojin Japan

“Waɗanda ke cikin motar sienna su ma sun ƙone, babu wanda ya tsira.

“Wata mota da aka ajiye a kusa da wurin da lamarin ya faru ita ma ta kama wuta a yayin da lamarin ya faru kuma ta ƙone ƙurmus.

“Gobarar da ta kama motocin ta kuma lalata wani gida da ke kusa da wurin da wutar ta tashi.

“Har yanzu ba mu tabbatar da wani wanda ya tsira da ransa ba a duk cikin waɗanda lamarin ya rutsa da su,” in ji Adejo Usman, wani mazaunin Aloma.

Ya ce mutanen ƙauyen ba su iya yin komai don ceto wasu fasinjojin da suka maƙale saboda babu kayan ceton gaggawa da za a iya kuɓutar da su.

Kwamandan sashin hukumar kiyaye haɗɗura ta ƙasa (FRSC), Samuel Ayedeji, ya ce yana cikin wani taro lokacin da aka tuntuɓe shi kan lamarin.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like