No menu items!

Sample Page Title

Date:

Aƙalla ɗalibai biyu na wata makarantar sakandare da ba a bayyana ba da ke unguwar Gwarinpa a Abuja, an yi zargin jami’an hukumar tsaro ta NSCDC ya harbe su har lahira.

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 11:30 na safiyar ranar Laraba, 29 ga watan Nuwamba yayinda aka tura jami’an NSCDC da ke ofishin babban birnin tarayya Abuja domin samar da tsaro a yayin gudanar da jarrabawar.

Rikicin ya haifar da hargitsi a kusa da harabar makarantar amma jami’an ‘yan sanda da suka isa wurin sun cafke jami’an NSCDC tare da kwantar da hankula.

KU KUMA KARANTA: Kwamishinan ‘yan sandan Kano ya bada umarnin kamo sufeton da ya harbi mutane uku a Kurna

Kakakin rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, Josephine Adeh, ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce, “An samu wani lamari a wata makarantar sakandare. Nan take muka je wurin, kuma a halin yanzu, ina iya tabbatar da cewa an dawo da zaman lafiya a yankin”.

Adeh ta ce kwamishinan ‘yan sanda na babban birnin tarayya Abuja, Garba Haruna ya bayar da umarnin gudanar da bincike domin sanin yadda lamarin ya faru.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...